GENOTYPE A MUSULUNCI TARE DA BINCIKEN MASANA KASHI NA UKU (3)

GENOTYPE A MUSULUNCI (3)

*

A rubutun farko da na biyu, mun fahimci asalin samuwar mutum a fuskar musulunci da fuskar kimiyya, mun fahimci menene muhimman abubuwan da genotype ya ƙunsa da kuma maniyyi da abinda ya ƙunsa.

 

A wurin yan kimiyya, genotype shine alamu na launin protein da ake samu a cikin RBC (red blood cell), sun raba genotype gidaje daban-daban daga biyar zuwa ashirin da wani abu gwargwadon binciken su akan “haemoglobin” wanda ake samu a RBC, mafi shahara sune AA, AC, AS, CC, SC da kuma SS.

 

Sun tabbatar cewa mutane masu genotype din SC da SS sune masu cutar sickle cell (sikila), kuma babu makawa muddin iyaye suna da wannan genotype din (ko AS wanda ake tsammanin zasu haifar da sikila) suka yi aure, yara sikila zasu haifa, kawar da haka kuwa sai dai suyi amfani da “In vitro fertilization” wurin samar da ciki, ko kuma a kwashe jini da ɓargon mai cutar, a musanya da lafiyayyen jini da ɓargo.

 

A MUSULUNCI KUWA

 

Dole ne dukkan mumini ya yarda da

وما تحمل من أنثى ولا تضع إلا بعلمه

Wato “babu macen da zata dauki ciki ko ta haife cikin sai da sanin sa (Allah)”. Shiyasa za kaga wasu wayanda Allah bai nufa da samun haihuwa ba, in suka je asibiti sai likitocin suce tabbas lafiyan miji da matan kalau, to in lafiya suke me ya hana samun cikin?

 

Bayan iznin Allah a harkar haihuwa, sai matakin samun cikin, wanda ya fara daga fitar Maniyyi (نطفة) daga namiji zuwa shigar ƙwayar maniyyin (سللة) cikin mace inda zasu hadu da ƙwayar haihuwar mace su zama (نطفة امشاج), daga nan Allah (da kansa) zai mayar dashi gudan jini, ya mayar dashi tsoka, ya fidda mashi siffofi, ya busa masa rai, ya bashi alqawari sannan a haife shi, (kamar yadda yazo a wurare da dama a Alqur’ani).

 

Tabbas Annabi SAW ya hori al’umma da zaben uwa ta gari, domin yaro yana gadon halayya da suffa da cuta (irin kuturta) daga iyaye musamman uwa, amma kuma Allah da Annabi sun nuna abubuwan dake haifar da samun ya’ya marasa lafiya ko muni ko rashin tarbiyya da albarka, daga cikin su akwai:

 

1. IKON ALLAH: Domin jarraba imanin mumini, Allah yakan fitar da rayayye daga matacce kuma yakan fitar da matacce daga rayayye, kamar yadda ya jarrabi Annabin sa da samun “kana’ana”.

 

2. CIN HARAM: Hadisai mabanbanta sunyi nuni da illar haram ga JIKI da IMANIN musulmi, har a wani hadisin ma Annabi SAW ya nuna addu’ar mutum maciyyin haram bata karɓuwa, kuma maniyyi ana samar dashi ne daga abincin da iyaye suka ci, Idan har haram zai hana addu’ar ka karɓuwa, me zai sa ya kasa gurɓata maka ƙwayoyin haihuwar ka?

 

3. SHAIDANI: Annabi SAW ya tabbatar akwai shaidanin aljani wanda yake saduwa da matar mutum yayin da mijin nata yake saduwa da ita muddin bai yi addu’a ba kafin ya fara jima’in, kuma tare da aljanin zai saki maniyyi a cikin matar tashi, haduwar maniyyin aljanin da nasu zai sa su haifi yaro mara lafiya ko mara jin magana da sauran su.

 

MAFITA

1. ABINCI: Kwayoyin haihuwa suna samuwa ne daga abinci, shiyasa a hadisai mabanbanta Annabi yayi nuni da tasirin dabino, zuma da nono ga lafiyar jikin mutum, musamman mace mai ciki, cin dabino sau uku da safe, yana sa mace ta haifi yaro lafiyayye kuma kyakkyawa.

 

2. MAGANI: idan kuna da mutum mai fama da cutar sikila, turawa basu da magani, Amma Annabi SAW yana da magani, ya tabbatar a hadisi cewa Suratul Fatiha tana maganace kowacce irin cuta, Imam Nazifi Alqarmawiy Kano ya kawo fa’idar fitsarin raqumi daga Annabi SAW. Malaman lafiyar musulunci sun tabbatar rubuta suratul fatiha sau 41 a wanke da ruwan zam-zam (3 litres) a zuba fitsarin raqumi (murfin bottle water) guda uku, a sha da safe minti 15 kafin a ci abinci, za a warke daga cutar sikila ko wanin sa wanda ya shafi kwayoyin halitta da IZNIN ALLAH.

 

DAGA KARSHE

Mai hankali zai fi gaskata turawa saboda a zahiri suna da na’ura kuma suna gwaje-gwaje, amma kar ka manta a gwaje-gwajen nasu ne suka zurfafa har suka saɓawa addinin ka. A wurin su asalin mutum ba yadda Ubangijin ka ya fada suka yarda ba, basu yarda da illar haram ko tasirin halal ba, basu yarda da shafar aljanu ko sihiri ko maita ba, basu yarda wani abu zai iya faruwa ko rashin faruwa bisa iznin Ubangijin ka ba.

 

ABINDA AKE GUDU AKA HANA MUSULMI ZIYARTAR BOKAYE DON KAR SU YARDA WANI HALITTA NE YA HANA SU KO YA BASU WANI ABU BA DA IZNIN ALLAH BA, YANA FARUWA DA JAMA’A DA YAWA SABODA ZIYARTAR MASU KIMIYYAR TURAWA, SUNA GANIN AMSAR KIMIYYA GA MATSALOLIN SU ITACE MAFITA TA KARSHE BA QUDURAR ALLAH BA.

 

Note: Bana jayayya da kowa, nayi rubutun nan ne don in karfafi imanin musulmai kawai.

 

✍️ Sidi Sadauki

Share

Back to top button