KISSA: Kissan Sheikh Dahiru Usman Bauchi RA Da Wasu Jikokin Sa.

Wasu Kananan Yara Daga Cikin Jikokin Maulana Sheikh Dahiru Usman Bauchi Suka Aikata wani karamin Laifi su Uku Ana Sallah sai Suka Kunna Famfo sunata Wasa da Ruwa Bayan Idar da Sallah sai Maualana Sheikh yasa

 

Aka kirawosu gabansa yace a samo bulala sai yace dasu meye yasa ana Sallah Kuna Wasa sai Suka kasa magana sai Shehu yace ya’yan waye sai a kace Akaramakallh dan-wane -ne da Dan wane Cikin ya’yan Maualana Sheikh sai maulana Sheikh yace meye Sunanku sai daya.

 

Yace sunana Muhammadu dayan yace Ahmad Tijjani dayan yace Ibrahim Inyass sai babu bata lokaci Shehu yace dasu Ku tashi ku tafi kunci Albarkacin masu Sunanku ko sunana Shehu Ibrahim Inyass R T.A. Shehu baya iya kira haka

 

Gatsau sai dai Idan karatu ya biyo takai shiyasa ma yake Kiran khadimul Faida da Suna Shehu saboda takwarane ga Shehu Ibrahim Inyass R.T.A. to bari Kuma Shugaban Halitta Annabi Muhammadu S.A.W.. yakamata a kula Allah ya kiyaye mana Imanimmu don Alfarmam Annabi Muhammadu S.A.W.

 

Daga: Abubakar Ibrahim Wunti

Share

Back to top button