KISSA: Kissar Wata Mata Tsohuwa A Zamanin Manzon Allah SAW.

A Zamanin ANNABI (S.A.W) anyi wata mata tsohuwa mai masifar rikici da raki, ita wannan mata ta kasance kullun saita kawo kara gurin ANNABI (S.A.W) cewa anyi mata kaza, ko tace masa yara sun takura mata.
Ana cikin haka wata rana ta shigo gidan ANNABI (S.A.W) domin takai masa kara, tana shiga saita tarar da killishi a gabansa, sai tace menene wannan sai yace mata kilishi ne, bayan ta gaya masa matsalarta, kafin ta tashi sai ya dauko kilishin yace ga wannan naki ne
.
Sai wannan tsohuwa tacewa fiyayyen halitta, kaga bakin nawa babu hakora bazan iya taunawa ba,
.
Sai ANNABI (S.A.W) ya karbi kilishin ya saka a bakin sa, ya ciccira mata yadda zata iya taunawa,
.
Sannan sai ANNABI (S.A.W) ya mika mata Tsohuwa ta dauki kilishin ta fara ci
.
A take a wurin sai anji ta fara yin salati ga ANNABI (S.A.W)
.
Bayan kwana biyu sai daya daga cikin matan ANNABI (S.A.W) suke tambaye shi cewa:
.
Ya ANNABIN ALLAH yanzu wannan tsohuwar sai dai kawai ta shigo gidan tana salati kawai, kuma ta gaishemu ta koma, amma ta daina kawo karar kowa?
.
Sai ANNABI (S.A.W) yace kun manta da
ranar dana bata kilishi?
.
Sai matan suka ce kwarai kuwa mun tuna da wannan Ranar!
.
Sai ANNABI (S.A.W) yace to ai Albarkar nyawun dake bakina ne wanda ya taba
kilishin Shine ALLAH ya kawar mata da duk wata damuwan ta anan duniya.
.
Kaji fiyayyen halitta kenan. Umar chobbe ne ke gaisheka Ya Rasulullah
.
YA ALLAH ka BAMU ALJANNA ALBARKAN NYAWUN BAKIN ANNABI MUHAMMAD (S.A.W).
.
Ya Allah kasa Albarkan Nyawun ANNABI S.A.W Ya Kawar Mana da Dukkan Damuwanmu Duniya da lahira Muma Bijahi S.A.W. Amiin