MURNA DA RANAR HAIHUWAR ANNABI ISAH (ALAIHIS- SALAM) Tare Da Sheikh Al-Habib Aliy Al-Jafriy.

MURNA DA RANAR HAIHUWAR ANNABI ISAH (ALAIHIS- SALAM)

 

Sheikh Al-Habib Aliy Al-Jafriy

 

Tarjama: Saleh Kaura

 

Godiya ta tabbata ga Allah, wanda shi ne yake fadi a cikin littafinsa da bata ba ta iya kusantarsa ta kowace hanya, saboda mai cikakken hikima, mai kuma yawan yaba wa bayinsa da suka yi aiki na kwarai ne ya saukar da shi, yana cewa:

 

“والسلام علي يوم ولدت…..”

 

Ma’ana: ((Aminci ya tabbata a gare ni a ranar da aka haife ni)) [Maryam: 33].

 

Tsira da aminci su tabbata ga shugabanmu Annabi Muhammadu, wanda shi ne yake fadi a cikin ingantaccen Hadisi cewa: “Mu ne muka fi su kusa da Annabi Musa…”, haka Annabi (SallalLahu alaiHi wa Alihi wa sallam) ya fadi lokacin da aka ce masa Yahudawan Madina suna azumtar ranar Ashura saboda su nuna farin cikin su da tseratar da Annabi Musa (AlaiHis Salam) da mutanen sa daga sharrin Fir’auna da rundunar sa, da ma can yana azumtar wannan rana tun yana garin Makka kafin hijira… Manzon Allah (SallalLahu alaiHi wa Alihi wa sallam) bai tambayi dangantakar faruwan haka da watannin Larabawa ba, duk kuwa da cewa akwai bambanci watannin na Larabawa da kirgan watannin Ibraniyyanci, kawai ya gamsu da cewa Yahudawan Madina suna amfani da watannin Larabawa; sakamakon zaman su tare da su, bai ce: ta yaya aka tabbatar da ingancin ranar ba, don Yahudawa sun sauya littafinsu, saboda haka bai halatta mu amince masu wajen bayyana ranar da aka tseratar da Annabi Musa (AlaiHis Salam) ba?! Domin al’amarin ba wai yana rataye da lokaci ba ne, yana rataye ne da ma’anar da wannan rana take dauke da ita, wadda ita ce murna da farin ciki da falalar da Allah ya yi wa al’umma, da kuma nuna soyayya ga salihan bayin Allah.. Lallai wannan dangantaka da lokutan da Allah ya yi wa salihan bayinsa falala dangantaka ce da take da asali mai karfi a cikin addinin mu..

 

Rukunin Musulunci na biyar wanda shi ne Hajji cike yake da dangantaka da falalar Allah da ya yi wa zababbun salihan bayinsa na cikin al’ummomin da suka gabace mu.. fara tun daga dawafin da ake yi a Ka’aba, wanda Annabi Ibrahim da dansa Annabi Isma’il (AlaiHimas Salam) suka kyautata gininsa, hada da sassarfar da ake yi tsakanin dutsen “Safa” da “Marwa”, inda Sayyidatuna Hajara –Bamisriya- ta yi ta kai-komo tsakanin wadannan duwatsu guda biyu, tana neman ruwan da za ta sha ita da jaririnta… ga kuma jifar “jamarat” a “Mina”, inda KhalilulLah (AlaiHis Salam) ya jefi shaidan lokacin da yake kokarin hana shi yi wa Allah Madaukakin Sarki biyayya a jarabawar da aka yi masa na yanka dansa Isma’il… ga kuma yanka “Hadaya” da yake tuna mana da babban abin yankan da Allah ya fanshi Annabi Isma’il (AlaiHis Salam) da shi, bayan mahaifinsa ya yi nasara a cikin wannan jarrabawa mai wahala… wannan shi ne girman ayyukan addinin mu, da muke bauta wa Allah Madaukakin Sarki da shi, rataye suke da dadaddun ma’anoni masu daraja, ba wai motsa jiki da ayyukan zahiri ne kawai ba… Allah Madaukakin Sarki yana cewa:

 

وذكرهم بأيام الله إن في ذلك لآيات لكل صبَّار شكور”

 

Ma’ana: ((Ka tuna masu da ranakun falalan Allah, lallai a cikin yin haka akwai ayoyi ga duk wani mai yawan hakuri da yawan godewa.)) [Ibrahim: 5].

 

Saboda haka ne, a duk sanda ranar da aka haifi Shugabanmu Annabi Isah (AlaiHis Salam) ta zagayo muke jin cewa mun zo lokaci ne da za mu tuna da ranakun da falalar Allah ta sauka ga bil’adama.

 

Allah ya ba shi wata babban ni’ima a wannan rana da aka haife shi, kuma wannan ni’ima tana da dangantaka na kut da kut da ZAMAN LAFIYAn da muke matukar bukatarsa a wannan lokaci…

 

Na’am, lallai Allah ya sanya Shugabanmu Annabi Isah ya zamo wata babban alama ta Zaman lafiya a wannan duniya… Ba shi ya fadi ta bakin Annabi Isah yana cewa:

 

“والسلام علي يوم ولدت ويوم أموت ويوم أبعث حيا” ba

 

Ma’ana: ((Aminci –Zaman lafiya- ya tabbata a gare ni a ranar da aka haife ni, da ranar da zan yi wafati, da ranar da za a tashe ni a raye)) ba? [Maryam: 33].

 

Wannan kawai ya isa ya sanya na yi farin ciki da wannan babban abin tunawa, ba tare da na waiwayi daidaiton yanda ranar take a wurin mu, ko a wurin wanin mu ba, ko sabanin da yake tsakanin “Arsazuks” da “Katolik” da “Burustaniti” ba, in dinga jayayya wajen haddade ranar da hakan ya faru ba… ba domin komai ba, sai don cewa al’amarin ba wai ya ratayu da ranar ba ne, a’a, yana rataye ne da ma’anar da ranar take dauke da ita…

 

Bugu da kari kuma, lallai ‘yan uwanmu a mutuntaka, da abokan zaman mu a kasa daya, da ‘yan uwan mu a halitta suna da hakki kyautatawa da na adalci a kan mu, hakkokin da Allah Madaukakin Sarki ya fadakar da mu zuwa gare su a inda yake cewa:

 

“لا ينهاكم الله عن الذين لم يقاتلوكم في الدين ولم يخرجوكم من دياركم أن تبروهم وتقسطوا إليهم إن الله يحب المقسطين”

 

Ma’ana: ((Lallai Allah bai hana ku sadar da zumunta da adalci ga wadanda ba su yaqe ku saboda addinin ku ba, ba kuma su fitar da ku daga gidajen ku ba, lallai Allah yana son masu adalci)) [al-Mumtahana: 8].

 

Al-Hasanul Basariy ya ce: Lallai wasu Musulmai sun nemi jin ta bakin Manzon Allah (SallalLahu alaiHi wa Alihi wa sallam) game da sada zumunci da ‘yan uwan su wadanda ba Musulmai ba, sai Alllah ya saukar da wannan ayar… Ibn Abbas ya ce: yana nufin sadar da zumunci da ma wanin sa, inda kuma ya ce:

 

“إن الله يحب المقسطين”.

 

Ma’ana: ((Lallai Allah yana son masu adalci)), Ana nufin masu sada zumunta da kyautatawa.. Shaihin masu Tafsirin Alkur’ani, Al-Hafiz Ibn Jarir at-Tabariy yana cewa –a lokacin da yake fassara wannan ayar-: maganar da tafi zama daidai ita ce maganar da take cewa: abin da ake nufi da haka shi ne: Allah Madaukakin Sarki bai hana ku sada zumunta da mutanen da ba su yake ku saboda addinin ku ba, na cikin dukan addinai, ku kuma kyautata masu mu’amala, ku kuma yi masu adalci… babu wata ma’ana ga maganar da take cewa: an share hukuncin wannan aya.. za ku iya lura da irin yanda Allah Madaukakin Sarki ya hada tsakanin kyautata mu’amala wa wadanda ba Musulmai ba da soyayyar sa, yana cewa:

 

“إن الله يحب المقسطين”.

 

Ma’ana: ((Lallai Allah yana son masu adalci)).

 

Kyautatawa da kuma yin adalci ga wadanda ba Musulmai ba, hanya ce da take kai wa zuwa ga soyayyar Allah Madaukakin Sarki… “abin da ake cewa da shi “al-Birru” shi ne kyawawan dabi’u, Kaman yanda Masoyinmu Zababben Allah (SallalLahu alaiHi wa Alihi wa sallam) ya bayyana..

 

*******

 

Kafin ‘yan uwana daliban ilimi su hayayyako mini, ko su tattaro magangannun malaman da suka hana a taya wadanda ba Musulmai ba murna a lokacin idin su… ina son in tuna masu da cewa: wadanda suka hana a taya wadanda ba Musulmi ba murna a ranakun idin su, sun hada hakan ne da tunanin kada a “tabbatar da su” akan abin da suka yi imani da shi, wanda kuma ya saba wa karantarwar Musulunci… ba su kawo dalili na karara da ya hana a taya su murnar ba…

 

Gaskiya wannan “Tabbatarwa” a wannan zamanin abu ne da ma bai taso ba a ce Musulmai sun yi masu, musamman bayan ilimin Musulunci ya yadu a ko’ina, an kuma san bambancin da yake tsakanin addinai, kuma komai yana bayyane a fili.. saboda a yanzu dai babu wani Musulmin da yake taya makwabcinsa Kirista murna a idin Kirsimeti da yake tunanin cewa hakan yana tabbatar da Kiristoci ne akan cewa Annabi Isah Allah ne, ko kuma dan Allah!…. haka ma babu wani Kiristan da yake tunanin haka ga Musulmin da ya taya shi murna! Kaman dai yanda babu wani Kirista da yake taya makwabtansa Musulmai murna da idin su, ko da watan Ramadan, ko watan Maulidin Annabi da yake tunanin cewa hakan yana nufin ya yi imani da abin da Musulmai suka yi imani da shi ne, ko yana tabbatar da su akan haka, babu kuma wani Musulmi da yake ganin cewa Kiristan da ya taya shi murna ya zama Musulmi, ko ya tabbatar da Musulmai akan abin da suke yi!..

 

Ma’anonin da suke isa zuwa ga zukata da hankula su ne sada zumunci da kyautatawa, da kuma kyautata dabi’u a mu’amala ta zamantakewa ..

 

Shin a wannan lokacin akwai wani mai hankalin da yake ganin haka a matsayin tabbatar da su a kan akidar su, ku nuna muna tare da su akan abin da suka yi imani?! Ko yin tarayya da su a wajen bauta?! Ashe mun kai wannan ci-bayan da za mu dinga caccakar juna, muna fitar da fatawa da bayanai, muna zagin juna da zargin juna, kai ma muna shakka akan imanin junan mu, kawai saboda kalamai masu dadi da Musulmi ya fada wa makwabcinsa Kirista: “Ina taya ka murna da wannan rana”? kai jama’a, da Allah wane kwazazzabo ne muke son mu auka da ‘ya’yan mu masu tasowa a ciki ne haka?! Wane irin rikon wulakanci ne muka yi wa girman wannan addinin namu wanda muke gabatar da shi ga matasanmu?.. Kai da ba ka son ka taya su murna, wannan hakkinka ne kada ka yi, da ma babu wanda ya ce maka hakan farilla ne, amma ka fito kana sukan wadanda suke yi, kana jifan su da kalamai marasa dadi, kana shigar da shakka akan asalin imanin su! To, ka sani wannan abu da kake yi shi ne wasa da addinin Allah! Shi ne kuma wulakantar da darajar wannan shari’ar da ta ginu akan rangwame da mutunci!..

 

Don Allah ku kame bakin ku, ku daina yin abubuwan da za su sanya a yi wa wannan babban addinin mummunan fahimta… don Allah ku daina kore mutane daga addini, da bakanta shi a wurin mutane ta hanyar kuntata farfajiyarsa mai fadi a gare su… ku tuna da fushi da kuma gargadi mai tsanani da Annabi (SallalLahu alaiHi wa Alihi wa sallam) ya yi a lokacin da aka kawo masa karar cewa akwai wani mutum da yake zuwa sallar Asubahi a makare, saboda limaminsu yana tsawaita karatu a sallah, Kaman yanda Imam al-Bukhari ya ruwaito daga Abu Mas’ud al-Ansariy, cewa: wani mutum ya ce: ya Manzon Allah, Lallai ina jinkirin fitowa sallar Asubahi ne saboda wane yana tsawaita mana sallah… Abu Mas’ud ya ce: Ban taba ganin Manzon Allah (SallalLahu alaiHi wa Alihi wa sallam) ya yi fushi a wurin wa’azi ba kaman na wannan ranar! Manzon Allah (SallalLahu alaiHi wa Alihi wa sallam) ya ce: “Ya ku mutane, lallai a cikin ku akwai masu kore mutane daga ayyukan alhairi, duk wanda zai yi wa mutane limanci, to ya takaita; ku sani cewa a cikin su akwai mai rauni, da tsoho, da mai wata bukata”.

 

Annabi (SallalLahu alaiHi wa Alihi wa sallam) ya yi fushi mai tsanani a wannan wa’azi nasa, abin da har ya kai ga ya tuhumi mai tsawaita wa mutane a wajen sallah da cewa “yana kore mutane daga ayyukan alhairi”!… to, ina kuma ga mutumin da yake sukan mutane a cikin imaninsu, yana kafirta su saboda kawai sun kyautata wa makwabtan su?!

 

Ina son in tuna wa kai na, kuma in tuna maku da wasiyyar Manzon Allah (SallalLahu alaiHi wa Alihi wa sallam) da take cewa: “Ku saukaka kada ku tsananta, ku yi albishir kada ku kore mutane”….

 

A karshe…

 

Ina taya Shugabanmu Annabi Muhammadu (SallalLahu alaiHi wa Alihi wa sallam) murna da ranar haihuwar Annabi Isahh (AlaiHis Salam)..

 

Na’am, ina taya Shugabanmu Annabi Muhammadu (SallalLahu alaiHi wa Alihi wa sallam) murna….

 

Ba shi ne ya ce: “Ni ne na fi kusa da Annabi Isah dan Maryam a duniya da lahira ba..”…?!

 

Ina taya Musulmai da Kiristoci –da ma daukacin bil’adama- murna da haihuwar Annabi Isah (AlaiHis Salam), wanda ya bayyana wa duniya, yana dauke da ma’anar sunan Allah “as-Salam”, hakan ya sanya ya zamo babban alama ta zaman lafiya da aminci..

 

Ina kuma fada wa Shugabanmu Annabi Isah (AlaiHis Salam):

 

Ya Shugabana, ya Ruhin Allah da kalmarsa…. Amincin Allah ya tabbata a gare ka ranar da aka haife ka, da ranar da za ka yi wafati, da ranar da Allah zai tashe ka a raye.

 

Sheikh al-Habib Aliy al-Jafriy (HafizahulLah)

 

Tarjama: Saleh Kaura. 25/12/2016

Share

Back to top button