Takaitaccen Tarihin Sheikh Ahmad Tijjani RA Shugaban Waliyai Kashi Na Goma Sha Uku (13).

CIKAMAKIN WALIYAI (13)

 

FALALAR DARIKAR TIJJANIYYA

 

Bayan Annabi SAW ya yiwa Shehu Tijjani RTA iznin bayar da wannan Ɗarikar, sai Shehu Tijjani ya rubuta wasikar neman Alfarma ga Annabi SAW saboda shi ba zai iya kallon Annabi ido da ido ya dinga magana yadda yaso ba saboda kunya da ladabi.

 

A wasikar yana cewa:

 

Ina neman Alfarma daga gareka ya Manzon Allah SAW ka tabbatar min ni da dukkan wayanda suka rayu cikin wannan Ɗariƙar, mutuwa da cikakken imani, Ina rokon Allah Madaukakin Sarki ya kiyaye mu daga azabar sa, da tsoro da firgici da firgita da dukkan sharri, daga lokacin mutuwa har zuwa lokacin da muka tabbata a gidan Aljannah, ya kuma gafarta mini da su dukkan zunuban mu da suka gabata baki daya da wayanda za muyi masu zuwa. Ina rokon Allah Maɗaukakin Sarki Ya lullube mu da Al’arshin sa ranar kiyama, kuma ya shayar da mu a tafkin Shugaban mu Manzon Allah SAW. Ina rokon Ubangijin mu ya shigar da mu Aljanna ba tare da hukunci ko Azaba ba, ya sanya mu a rukunin farko na masu shiga Aljanna kuma ya tabbatar damu a cikin Firdausi da Adnan. Ina kuma roƙon Manzon Allah SAW ya tabbatar min da dukkan abin da aka ambata a cikin waɗannan wasika gareni da dukkan sahabbai na, Allah ya amshi abin da na roƙa gaba ɗayansa”

 

Daga nan aka isar da wannan rubutu zuwa hannun Manzon Allah SAW mai albarka a farke ba a mafarki ba, Annabi SAW ya amsa masa da cewa: “Ka sani na tabbatar da dukkan buƙatun da ke cikin wannan wasiqar, tare da alqawari gare ka da su, har sai kun kasance tare da ni a matsayi mafi girma na Iliyin, Wassalamu Alaikum.”

 

Bayan mutuwa cikin imani da shiga aljanna babu hisabi, a duniya akwai falalar samun Muƙamin ƙudubaniyya daidai da ƙuɗubai dubu daya ga duk mutum ɗaya wanda ya karbi darikar Tijjaniyya, Alhamdulillah.

 

FA MU MABIYAN KA MUN SAMU

WA KEDA UBA KAMAR NAMU

DARIKA BA KAMAR TAMU

ANA WURIDI KAMAR NAMU

FA BABU KAMAR KA TIJJANI

 

✍️ Sidi Sadauki

Share

Back to top button