Yana Zargin Wasu Bata-garin Sojojin Najeriya Da Kashe Fitaccen Malami A Gashua.

Inna’lillah Wa’inna Ilaihir Raji’un 😭😭

 

…Yana Zargin Wasu Bata-Garin Sojojin Najeriya Da Ka@she Fitaccen Malami A Gashua.

 

A jiya Asabar ne muka samu labarin rasuwan babban malamin Musulunci a jihar Yobe Sheikh Goni Aisami dake garin Gashua a jihar Yabe rasuwa a hanyar dawowa daga jihar Kano zuwa Gashua.

 

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya nuna Damusan sa akan faruwan lamarin tare da nuna baÆ™in-cikinsa akan ki@san da Akayi wa Sheikh Goni Aisami, a ranar Juma’a.

 

BBC Hausa sun ruwaito cewa malamin mazaunin garin Gashua da ke karamar hukumar Bade an zargi sojoji da harbe shi a yankin Jaji-Maji da ke karamar hukumar Karasuwa na jihar Yobe.

 

Kakakin ‘yan sandan jihar, Daungus Abdulkarim, ya ce sojojin biyu da suka yi kokarin sace motar malamin bayan harbe shi an damÆ™esu.

 

Gwamna Buni a wata sanarwa da ya fitar a Damaturu, ya ce wannan kisa abin takaici ne da alla-wadai, don haka za a binciki lamarin.

 

Mai Mala ya ce duk wanda aka samu da laifi za su fuskanci hukunci. Sannan ya miÆ™a ta’azziyarsa zuwa da iyalan marigayin da al’ummar karamar hukumar Bade da ilahirin jihar kan kisan Aisami.

 

An gudanar da sallar jana’izan sa kamar yadda addinin Islama ya tanadar a garin Bade dake karamar hukumar Gashua jihar Yobe.

 

Allah ya jikan sa da rahma ya gafarta masa rahma ya karbi shahadar sa. Amiin Yaa ALLAH

 

Babangida A Maina

Tijjaniyya Media News

Share

Back to top button