ADDINI

  • Matashin Daya Musulunta Ya Zama Cikakken Malamin Islamiyya Har Ya Fara Rubuce Alkur’ani.

    Matashin daya Musulunta ya zama cikakken malamin Islamiyya har da rubuce Al’Qur’ani.

     

    Daga Abdulnasir Yusuf Ladan

     

    Bayan na shiga ajin su (Faslu Imamu Malik Bin Anas) sai na tarar da shi ga Qur’anin sa a gefe yana ta fafatawa cikin kwanciyar hankali wajen yin wannan rubutun, sai na tsaya cak cike da farin ciki ina kallon ikon Allah.

     

    Wannan matashin da kuke gani sunansa Ibrahim, uma sunan mahaifinsa Sylvester watanni biyar baya a Karamar Hukumar Birnin Gwari Jihar Kaduna, ko harafin Alifun baya iya furtawa balantana ya rubuta, cikin ikon Allah bayan shigarsa Islamiyyarmu ta At-tatbiqul Islamiya, yau gashi AlQur’anin ma yake kokarin ya rubuce shi duka.

     

    Bugu da ƙari har Majiyar mu ya ƙara tabbatar mana cewa; akan iya bashi dama don ya shiga wani aji ya basu Karatu gwargwadon abinda ya sani, kuma cikin ‘yan waɗanan lokacin ƙanƙani.

     

    Allah ya kara masa himma. Amiiiin

    Share
  • Masha’Allah; Duk Wanda Ya Sanyawa Dan’sa Sunan Muhammadu Don Neman Albarkan Mai Suna Mahaifin Da Dan Duk Suna Aljannah.

    ABI UMAMATAL BAAHILI(R.A) YA RUWAITO DAGA ANNABI(S.A.W) Cewa;

     

    “MAN WULIDA LAHU MAULUDUN FA SAMMAHU MUHAMMADAN TABARRUKAN BIHI KANA HUWA WA MAULUDAHU FIL-JANNATI”.

     

    MA’ANA:

     

    “Duk Wanda Aka Haifa Masa ‘DA Ya Sanya Masa Suna ‘MUHAMMADU’ Don Neman Tabarruki Da Sunan Da Baban Da Abin Haihuwar Duk Suna Aljannah”.

     

    (REFERENCE: HALATU AHALUL HAQIQATI MAALLAHI; SIDI AHMAD AR-RUFAI AL-KABIR, PAGE:108,

    Shamsuddeen Az-Zahabi Ya Ce Hadisi Ne Mai Kyau,

    Mizanil Itidaal Imamul Muhaddisina Suyudi Ya Ce: Isnadinsa Ingantacce Ne: Mukhtasirul Maudu’at).

     

    TIRQASHI WA YA SAMU IRIN WANNAN GIRMAN IDAN BA SHI BA:’ MUHAMMADUR RASULULLAH’

    AKWAI SHI???

     

    BABU…. BABU……. BABU…….

     

    ALLAH KA BA MU ALBARKACIN SIRRIN DAKE TATTARE DA WANNAN SUNAN, ALBARKACIN MAI SUNAN(S.A.W) AMEEEN.

    Share
  • A Bisa Hankali Da Al’adar Zamantakewa JINI Ko FITSARI/BAWALI Najasa Ne, To Amma Al’amarin Ba Haka Yake Ba, Akan Na MANZON ALLAH(S.A.W).

    JINI Ko BAWALI/FITSARI;

     

    A Bisa Hankali Da Al’adar Zamantakewa JINI Ko FITSARI/BAWALI Najasa Ne (Musamman a Duniyar Musulmai An Tabbatar Da Cewa; JINI Ko FITSARI Da BAWALI Najasa Ne),

     

    Kuma Ta Fuskar Malaman Lafiya (Likitoci) Guba Ne, Na Kowa Haka Yake,

     

    To Amma Al’amarin Ba Haka Yake Ba, Akan Na MANZON ALLAH(S.A.W), JININSA Da BAWALINSA Ba Najasa Bane,

     

    Saboda Me???

     

    Saboda Suna Da Dangane/Alaqa Da MANZON ALLAH(S.A.W), Hasalima An Sha Su An Samu Lafiya, An Warke Sumul,

     

    Karatun Da Nake So Na Fitar Anan Shi Ne; Duk Abinda Yake Da Dangane/Alaqa Da MANZON ALLAH(S.A.W), To Yafi ‘Karfin Kushe Ko Muzantawa Komai ‘Kankantarsa, Ko Rashin Tsarkinsa a Gare Mu, Don Haka Ne;

     

    IYAYEN MANZON ALLAH(S.A.W),

    IYALAN MANZON ALLAH(S.A.W),

    MATAN MANZON ALLAH(S.A.W),

    SAHABBAN MANZON ALLAH(S.A.W),

    KAYAN MANZON ALLAH(S.A.W),

    DABBOBIN MANZON ALLAH(S.A.W),

    GARIN MANZON ALLAH(S.A.W),

     

    Da Sauransu,

     

    Duk Sun Fi ‘Karfin a Ta6a Su, Ko a Muzanta Su Saboda Suna Da Nasaba Ta Kai Tsaye Da MANZON ALLAH(S.A.W).

     

    Don Haka Masu Ta6a Mutumcin IYAYEN ANNABI(S.A.W) Sai Ku Shafawa Kanku Ruwa, Ku Kiyaye.

     

    Kun Ji Dai FITSARI/BAWALI Ko JININ MANZON ALLAH(S.A.W) Ma Yafi ‘Karfin Muzantawa Balantana IYAYEN ANNABI (S.A.W).

     

    Ku Ji Abinda QADHI IYAD Ya Ce;

     

    “KO FITSARIN DABBAR DA ANNABI (S.A.W) YAKE HAWA, IDAN MUTUM YA CE FITSARIN WARI YAKE, TO HUKUNCIN SHI KISA NE!”

     

    – (QADHI-IYAD MAI ASHIFAH SHI YA RUWAITO HAKAN).

     

    ALLAH KA ‘KARA TSARE MANA IMANINMU DAGA RUDANIN ZAMANI, YA ‘KARA MANA ‘KAUNAR SAYYIDUL-WUJUDI (S.A.W) AMEEEN

    Share
  • Soyayyar Annabi Ta Samarwa Wasu Daga Cikin Halittu Darajoji Da Muqamai A Wajen Allah Ba Tare Da Sunyi Sallar, Azumi Da Zakkah Ba.

    A cikin Tarihin ANNABI S.A.W An samu halittu da dama wadanda suka samu darajoji da muqamai awajen Allah da ANNABI S.A.W ba tare da sun taba yin sallah ko azumi, ko kuma wani aikin ibada ba, Sai dai Domin sun nuna SOYAYYARSU GA ANNABI S.A.W

     

    MISALI

    DUTSEN UHUDU:- ANNABI S.A.W yana cewa “Uhud dutse ne Wanda YAKE SONMU muma kuma MUNA SON SHI”. Kunga kenan dutsen Uhudu ya samu babban rabo.

     

    A KUTUTTUREN DABINO:- Wanda yayi kuka saboda tsananin Shauqi da Qaunar ANNABI S.A.W Kuma ANNABI S.A.W ya yarda dashi

     

    Gashi anan duniya amma yana chan Annabi ya dasa shi agidan ALJANNAH.

     

    BURAQAH:- Wacce ya hau adaren ISRA’I DA MI’IRAJI Ta kasance acikin ‘Yan uwanta Burakoki, amma ta rame bata ci bata sha saboda tsananin Bege da tunanin ANNABI S.A.W. Shiyasa Mala’ika Jibreel (AS) ya zabo ta ya taho da ita domin taga MASOYINTA ANNABI S.A.W. Kuma kafin ya hau bayanta sai da ta nemi wasu alfarmomi guda biyu awajensa ANNABI S.A.W. TACHE: “Ya Jibreelu ka gaya ma Wannan Masoyi, ma’abocin fuska mai kyau da Qyalkyali, INA SO YA SANYA NI ACIKIN CETONSA.. KUMA INA SO YA LAMUNCE MIN IN ZAMA ABIN HAWANSA AFILIN ALQIYAMAH”. Nan take ANNABI S.A.W yace “NA LAMUNCE MIKI”.

     

    KOGON DA YA SHIGA: Aranar yakin Uhud Har yanzun nan Kogon yana Qamshin jikin ANNABI S.A.W.

     

    QISSAR MUTUMIN NAN: mashayin giya wanda aka yi masa haddi har sau biyu. Da yazo akaro na ukun sai Sayyiduna Umar zai tsine masa. Sai ANNABI S.A.W yace “KYALE SHI YA UMAR. HAKIKA SHI YANA QAUNAR ALLAH DA MANZONSA”..(SAWW).

     

    ALLAH SHI QARA MANA SON ANNABI S.A.W YA SAMU A CIKIN CETONSA (S.A.W). AMIIN

    Share
  • Lokacin da Annabi SAW da Sayyaduna Abubakar suka shiga Madinah, sai mutanen garin suka karbe su hannu bibbiyu.

    HIJIRAR ANNABI (S.A.W) ZUWA MADINAH

     

    Sai Annabi (S.A.W) da Abubakar (R.A) suka nufi kogon Saur suna masu hijira zuwa Madinah, suka zauna cikin kogon tsawon kwanaki uku, don haka labarinsu sai ya bace wa kuraishawa. Lokacin da Annabi da Abubakar suka shiga Madinah, sai mutanen garin suka karbe su hannu bibbiyu, sai Annabi ya gina masallacinsa da masaukinsa.

     

    YAKUKUWAN DA ANNABI (S.A.W) YAYI A RAYUWARSA:

     

    An karbo hadisi daga “Ibn Abbas” (Allah ya kara masa yarda) yace: ”lokacin da Annabi ya fita daga garin Makka yana mai hijira,

     

    Sai Abubakar (R.A) yace: wadannan mutane (kuraishawa) sun shiga uku sun lalace!! Ta yaya za’ayi su fitar da Annabinsu daga garinsa!!

     

    Sai Allah madaukakin sarki ya saukar da fadinsa cewa: “An yi izini ga wadanda ake yakarsu da cewa lalle an zalunce su, kuma lallai hakika Allah mai iko ne kan taimakonsu” .[suratul Hajji, Aya :(39)].

     

    Itace aya ta farko data sauka tana umarni da yaki.

     

    Yakukunan da Annabi (S.A.W) yayi a rayuwarsa guda Ashirin da bakwai(27) ne, wadanda yaki ya faru a cikinsu guda tara(9) ne, gasu kamar haka:

     

    1.Badr.

    2.Uhud.

    3.Muraisi’i.

    4.Khandaq.

    5.Bani-kuraiza.

    6. Khaibar.

    7. Fathu-Makka.

    8. Hunain.

    9. Adda’if.

     

    Kuma ya aika Sariyyah (rundunan yaki karkashin jagorancin wani sahabi) guda hamsin da shida (56). Allah ya bamu Albarkacin sa bijahi S.A.W. Amiin Yaa Allah

    Share
Back to top button