Matashin daya Musulunta ya zama cikakken malamin Islamiyya har da rubuce Al’Qur’ani.
Daga Abdulnasir Yusuf Ladan
Bayan na shiga ajin su (Faslu Imamu Malik Bin Anas) sai na tarar da shi ga Qur’anin sa a gefe yana ta fafatawa cikin kwanciyar hankali wajen yin wannan rubutun, sai na tsaya cak cike da farin ciki ina kallon ikon Allah.
Wannan matashin da kuke gani sunansa Ibrahim, uma sunan mahaifinsa Sylvester watanni biyar baya a Karamar Hukumar Birnin Gwari Jihar Kaduna, ko harafin Alifun baya iya furtawa balantana ya rubuta, cikin ikon Allah bayan shigarsa Islamiyyarmu ta At-tatbiqul Islamiya, yau gashi AlQur’anin ma yake kokarin ya rubuce shi duka.
Bugu da ƙari har Majiyar mu ya ƙara tabbatar mana cewa; akan iya bashi dama don ya shiga wani aji ya basu Karatu gwargwadon abinda ya sani, kuma cikin ‘yan waɗanan lokacin ƙanƙani.
Allah ya kara masa himma. Amiiiin