ADDINI

  • DUK MUSULMAN NAJERIYA SUN GANE SU WAYE MAKIYA MANZON ALLAH SAW.

    DUK MUSULMAN NAJERIYA SUN GANE SU WAYE MAKIYA MANZON ALLAH SAW.

     

    ……Cewar Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Usman Bauchi RTA.

     

    Shugaban Gidauniyar Sheikh Dahiru Usman Bauchi, Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Usman Bauchi (Khadimul Faidha) Ya Bayyana Yanda Wasu Gaggan malaman Izala Suka Goyi Bayan Dan Uwansu Akan Kalman Batanci da Yayi Ma Fiyayyen Halitta Annabi Muhammadu ﷺ.

     

    Sheik Ibrahim Ya Kara da Cewa Bama Goyon Baya Wannan Al’amari Na Batanci ga Fiyayyen Halitta Annabi Muhammadu ﷺ,

     

    Ya Kara da Cewa ae Ba’a Raba Allah da Manzon Allah ﷺ, Raba Allah da Manzon Allah ﷺ Babban Laifi ne.

     

    Sannan Yayi Kira da Jan Kunne Wa Yan Uwa Masoya Manzon Allah ﷺ, da Cewa Kowa Yasan Inda Zai Na Sallar Ibada Don Allah Ba’a Raba shi da Manzon Sa ﷺ, Duk Inda Kaji Ance Allah to Zakiji Ance Manzon Allah ﷺ,

     

    Daga karshe Ya Yaba Ma Dukkanin Yan’uwa Musulmai Masoya Manzon Allah ﷺ, da Sukayi Tsayin Daka Don Kare Martaban Manzon Allah ﷺ, Yayi Addu’a Allah Ya Karfafi Musulunci da Al’ummar Musulmai Masoya Manzon Allah ﷺ,

     

    Kuma Ya Kara Kira ae ta Addu’a Allah Ya Kara Tona Musu Asiri a Duk Inda Suke, Mu kuma Allah Ya Karemu Daga Sharrin Makiya Manzon Allah ﷺ.

     

    Daga: Khadimul Faida Media Team Nigeria.

    Share
  • YANZU-YANZU: Mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubukar III Ya Tabbatar Da Ganin Jinjirin Watan Ramadan.

    YANZU-YANZU: Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar na uku ya sanar da ganin jaririn watan Ramadan na shekarar 2023 a wasu sassan Najeriya.

     

    Jerin Garuruwa 31 Da Aka Ga Jingirn Watan Ramadan A Najeriya.

     

    Jerin Garuruwa 31 Da Aka Ga Jingirn Watan Ramadan A Najeriya.

    (1) Rawayau jihar Katsina.”

    (2) Dutsin-ma Jihar Katsina.”

    (3) Kaduna Tarayyar Najeriya.”

    (4) Matari Zariya, Jahar Kaduna.”

    (5) Nguru Jahar Yobe.”

    (6) Ille-ife Jihar Osun.”

    (7) Legas Tarayyar Najeriya.”

    (8) Sanyinna Jihar Sokoto.

    (9) Zariya Jahar Kaduna.”

    (10) Kazaure Jihar Jigawa.”

    (11) Rimi Jihar Katsina.”

    (12) Mairua Jihar Katsina.”

    (13) Potiskum Jihar Yobe.”

    (14) Argungun Jihar Kebbi.”

    (15) Jahun Jihar Jigawa.”

    (16) Pambegua Jihar Kaduna.”

    (17) Illela Jihar Sokoto.

    (18) Pindiga Jihar Gombe.”

    (19) Minna Jihar Niger.”

    (20) Balangu, Kafin Hausa Jihar Jigawa.”

    (21) Jimeta Jihar Yola.”

    (22) Jalam Jihar Bauchi.”

    (23) Charanchi Jihar Katsina.”

    (24) Daura Jihar Katsina.”

    (25) Darazo Jihar Bauchi.”

    (26) Sansani Jihar Taraba.”

    (27) Obajana Jihar Kogi.

    (28) Porthscourt Jihar Riba.”

    (29) Turabu Kirikisanya Jihar Jigawa.”

    (30) Gololo Jihar Bauchi.”

    (31) Jos Jihar Filato.

     

    Allah ya bamu albarkacin wannan wata ALLAH yasa ayi lafiya. Amiiiin Yaa Allah

    Share
  • Jadawalin Malaman Tijjaniyya Da Zamu Kawo Maku Tafsir Alkur’ani Mai Girma Na Wannan Shekara 2023.

    2023 TAFSEER LIST OF TIJJANIYA SCHOLARS

     

    Sheikh Sharif Ibrahim Saleh

    Sheikh Dahiru Usman Bauchi

    Sheikh Halliru Maraya Kaduna

    Sheikh Prof. Ibrahim Maqary

    Sheikh Abdullahi Uwais Kano

     

    Sheikh Sani Khalifa Zaria

    Sheikh Shattima Almiskin

    Sheikh Modibbo Isah Shongo

    Sheikh Ibrahim Gajale

    Sheikh Tijjani Umar Titti

     

    Sheikh Dr. Atiku Balarabe Gusau

    Sheikh Khalifa Bashir Tijjani Z/Bare-Bari

    Sheikh Imam Mansur Kaduna

    Sheikh Dr. Arabi Abulfathi

    Sheikh Dr. Muneer Adam Katsina

     

    Sheikh Nazifi Alkarmawy

    Sheikh Harisu Salihu Jos

    Sheikh Abubakar Nasidi G/Dutse

    Sheikh Abubakar Madatai

    Sheikh Prof. Umar Sani Fagge

     

    Sheikh Hafiz Modibbo Chilo

    Sheikh Abdullahi Modibbo Tukur

    Sheikh Naziru Idris Gombe

    Sheikh Bashir Barhama Gombe

    Sheikh Malam Mai Nasara Zaria

     

    Sheikh Tijjani Umara Maiduguri

    Sheikh Imam Ghazali Funtua

    Sheikh Bello Mustapha Elmangary

    Sheikh Muhammad Nasir Shira

    Sheikh Dr. Mansur Makaranta

     

    Sheikh Mustapha Balarabe Gusau

    Sheikh Yusuf Lawan Funtua

    Sheikh Goni Ayuba Alkaramsamy

    Sheikh Isma’il Muhammad Bajoga

    Sheikh Dr. Kabiru Aliyu Tsafe

     

    Sheikh Dr. Bashir Dahiru Bauchi

    Sheikh Alaramma Sunusi Fiya Fiya

    Sheikh Dr. Yusuf Ali Gaya

    Sheikh Mustapha Adinga Alkusawy

    Sheikh Goni Ali Goni Saleh

     

    Sheikh Prof. Abubakar Yagawal

    Sheikh Sunusi Arzai Kano

    Sheikh Imam Junaidu Bauchi

    Sheikh Sunusi Godal Zamfara

    Sheikh Saleh Nuhu Sallau Kafinga

     

    Sheikh Muntaqa Modibbo Tukur

    Sheikh Abdullah Balarabe Gusau

    Sheikh Ahmad Muhammad Jinjiri

    Sheikh Khalifa Tijjani Harazumi

    Sheikh Tijjani Sheikh Dahiru

     

    Sheikh Salisu Musa Zaria

    Sheikh Zubayr Madigawa

    Sheikh Umar Gambo Sufi

    Sheikh Muhammad Kachalla

    Sheikh Dr. Nazifi Bichi

     

    Sheikh Ya-aqub Al-arab

    Sheikh Isma’il Bajoga Bauchi

    Sheikh Khalifa Abubakar K/Namoda

    Sheikh Abbas Ibrahim Saleh

    Sheikh Dr. Shehi Mai Jama’a

     

    Sheikh Dr. Ahmad Badwi Jigawa

    Sheikh Abubakar Sharif Umar

    Sheikh Abdullatif Modibbo Tukur

    Sheikh Prof. Abba Saleh Abdulfathi

    Sheikh Muhammad Waddu Shagamu

     

    Sheikh Abdulrahman Funtua

    Sheikh Habibu Dan Almajiri

    Sheikh Tijjani Kwadom

    Sheikh Barhama Damanda

    Sheikh Aliyu Jega Kebbi

     

    Sheikh Kamilu Minna

    Sheikh Muhammad Nasir

    Sheikh Munir Adam Koza

    Sheikh Abba Kuka Dabo

    Sharif Nasir Falaki Jos

     

    Sayyadi Abulfathi Sani Atijjany

    Sayyadi Nasir Ado Musa

    Sayyadi Hassan Adam Zaria

    Sayyadi Aliyu Cisse Ummahani

    Sayyadi Aminu Under 17

     

    Sayyadi Burhanuddeen M. Goje

    Sayyadi Aliyu Yaqub Misau

    Khadi Adamu Usman (Khadi)

    Sayyadi Abbas Sadauki Kano

    Sayyadi Muhammad Tutare

     

    Share
  • Yadda Azumi Yake A Wurin Bayin Allah Sufaye.

    AZUMI A WURIN SUFAYE

     

    Allah ya tabbatar da cewa abubuwa guda biyu babu wanda yasan adadin ladan su, sai shi kadai, sune HAQURI da AZUMI. Dalili kuwa, haquri da azumin duk suffar bayin sa ne waliyai, babu wanda kuwa yasan girman su a wajen sa, shiyasa ma in ka taba waliyyin sa, shi da kanshi zai yaqe ka.

     

    A bisa koyarwar Shari’a, Azumi shine kamewa daga ci, sha, kusantar iyali, nisantar ayyukan sharri da kuma qarfafa ayyukan alheri a cikin ranakun wata na tara (ramadan) a watannin arabiya, tsawon kwana 29 zuwa 30.

     

    Amma a wurin sufaye, azumi shine kamewa daga son zuciyar ka, zuwa abinda Allah yake so ta yadda yake so, a ko da yaushe.

     

    Wannan muqami ne na waliyai, wayanda ko da yaushe suke kokarin aikata abinda Allah zai ji dadi, da barin duk abinda zaisa Allah yayi fushi dasu. Ba kuma sai a cikin wata daya ba, A’a, kullum cikin haka suke.

     

    Kalmar azumi a larabci shine صوم (Saum).

    Harafin ص adadin sa shine 90, Harafin و adadin sa shine 6, adadin م adadin sa shine 40.

    90 + 6 + 40 = 136.

     

    136 din nan in ka juya shi zuwa haruffa, zai baka ولي (Waliy) wato waliyyi.

     

    Ko babu yawan azkarai da nafiloli, in ka kame kanka daga biyewa son zuciyar ka, zaka shiga sahun waliyan Allah ma’abota girman daraja.

     

    Dan haka yan’uwa, kamar yadda muke gasa da juna wurin tara abin duniya, ya kamata muyi fiye da haka wurin neman yardar Allah (wulaya).

     

    Amma matakin samun yardar Allah na farko, shine rashin cutar da halittun sa, da kuma yawan yafiya garesu in suka cuce ka, sai sanin sa sani na haqiqa, sannan kiyaye umurni ko hanin sa gwargwadon iko.

     

    Allah kasa mu fi qarfin zuciyar mu, ka bamu abin masarufi cikin wannan wata da za a shiga mai albarka, ka rufa mana asiri cikin ludufin ka, ka bamu ikon azumtar watan, idan munyi ka karɓa, domin darajar Madinah da wanda yake kwance cikin ta.

     

    ✍️Sidi Sadauki.

    Share
  • Annabi Muhammadu SAW Tare Da Dan’uwan Sa Annabi Dawood AS.

    ANNABI MUHAMMADU (S.A.W)

     

    In Kana Son Ganin Yadda ALLAH(S.W.T) Ya Fifita DARAJAR ANNABI(S.A.W) Fiye Da Ta Kowa, Dubi Yadda Ya Cewa ANNABI DAWOOD (A.S);

     

    “فَاحْكُم بَينَ النّاسِ بِالحَق”

     

    “Ka Yi Hukunci(Ya Kai Dawood) Tsakanin Mutane Da Gaskiya”,

     

    Amma a Haƙƙin ANNABI(S.A.W) Sai Ya Ce Masa:

     

    ” لِتَحْكُمَ بَينَ النّاسِ بِمَا أَرَاكَ اللَّهُ”

     

    “…Don Ka Yi Hukunci(Ya Muhammadu) Da Iyakar Abin Da Ka Fahimta Daga Allah”.

     

    Ya Yiwa ANNABI DAWOOD(A.S) Sharaɗi Na Ya Bi Gaskiya,

     

    Amma ANNABI MUHAMMADU(S.A.W) Ba Ai Masa Sharadi Ba, Sai Aka Ce Masa Da Iyakar Fahimtarsa Daga ALLAH(S.W.T).

     

    Sannan Ya Cewa ANNABI DAWOOD(A.S):

     

    وَلاَ تَتَّبِعِ الهَوَى فَيُضِلَّك عَن سَبِيلِ اللَّهِ.

     

    Wato: Ya Dawood Kar Ka Bi Son Zuciya; Ya Ɓatar Da Kai Ga Barin Hanyar ALLAH.

     

    Shi Kuwa ANNABI(S.A.W) Sai Aka Ce Masa:

     

    مَا ضَلَّ صَاحِبُكُم ..

    وَمَا يَنطِقُ عَنِ الهَوَى ..

     

    “Ai Sam Sam Muhammadu Bai Ta6a Ɓata Ba, Bai San Hanyar Ɓata Ba..

     

    …Sa’annan Kwata-Kwata Bai Ta6a Bi Ko Faɗin San Zuciya Ba”,

     

    Yayin Da Ake Hana ANNABI DAWOOD (A.S) Ya Kiyayi Bin Son Zuciya, Shi Ko ANNABI MUHAMMADU Tabbatar Wa Ake Yi Bai Ta6a Son Zuciyar Ba.

     

    Haka Nan Sanda Ake Ji Ma ANNABI DAWOOD (A.S) Tsoron Kar Ya Ɓata In Ya Bi Son Zuciyar Shi,

     

    Shi Kuwa MUHAMMADUR RASULULLAHI, Tabbatar Wa Ake Cewa Bai Ta6a Ɓata Ba, Bai San Hanyar Ɓata Ba, Tun Tale-Tale Har Abadal Abidin.

     

    صلوات الله وسلامه عليك يا حبيبي يا رسول الله.

     

    (©️Shehi Mai Jamaa✍️)

     

    ALLAH Ya ‘Kara Mana ƘAUNAR SAYYIDUL-WUJUDI (S.A.W). Amiiiin

    Share
Back to top button