AL’AJABI

  • GWANIN BAN SHA’AWA: Yadda Kananan Yara Suka Gudanar Da Mauludin Manzon Allah a Zariya. 

    GWANIN BAN SHA’AWA: Yadda ƙananan yara suka gudanar da maulidin manzo a Zariya.

     

    Daga Barista Nuraddeen Isma’eel

     

    “Wani abun ban mamaki na wasu ƙananan yara wanda duk cikarsu haifaffun garin Zaria ne jihar Kaduna, inda suka sabunta maulidin Fiyayyan halitta Annabi Muhammadu (SAW).

     

    “Shi dai wannan maulidin na ƙananan yaran sun saba gudanarwa a duk shekara kamar yadda rahoton hakan ke riskan Alfijir Hausa.”

     

    Yadda al’amarin maulidin ke tafiya cikin tsari da ƙayatarwa a halin yanzu haka, ganin yadda yaran ke gayyatar yayasu-yayasu Sa’o’in juna daga unguwanni daban-daba domin halartar wannan gagarumin Mauludin.

     

    “Rahoton na cigaba da bayyanawa kamar haka harda gagarumin walima da yaran ke shiryawa bayan kammala maulidin Fiyayyan halitta Annabi Muhammadu ( SAW).

     

    “Wannan maulidin ya gudanane a ranar juma’a 11/11/2022 a bakin kasuwanci Zariya cikin wani unguwa da ake kira a unguwar ƙarfe Gidan Hajiya ladi mai waina.”

     

    Allah ya saka masu da mafificin alkhairi, ya kara mana soyayyan Manzon Allah SAW. Amiiiin

    Share
Back to top button