DARIKA

  • Sheikh Ibrahim Inyass RA Ta Hanyarsa Sama Da Mutane Miliyan 30 Suka Karɓi Dariƙar Tijjaniyya. 

    KA SANI YA KAI MURIDI…

     

    Ɗariƙarmu ta Tijjaniyya, babu wanda yake da ikon cewa mallakinsa ce kuma babu mai iya barazanar korar kawai saboda wani saɓani ya haɗa ku. Shehin kowa a cikin wannan ɗariƙa Maulanmu Shehu Tijjani, ne Maulanmu Shehu Ibrahim Niasee, kuma shi ne babban Halifa a cikinta.

     

    Kabar tsayawa kula da masu danganta kansu da mallakar wannan ɗariƙa, suna ganin su ne kaɗai masu sanyawa ko hanawa. Sannan kar sake ka tsaya duban masu kaddamar Shehunan su a matsayin masu sanyawa ko kuma hanawa a kan abin da kwata kwata babu shi a cikin fikihun ɗariƙar ko dan suna ganin irin gudunmawar da suke bayarwa ga ɗariƙar Eh, gudunmawar da suke bayarwa na iya sanya su zama jiga-jigan wannan ɗariƙar amman ba masu sanyawa da hanawa ba.

     

    A tarihi babu wani malami da ya bayar da gagarumar gudunmawa ga wannan ɗariƙar da ma addinin musulunci kamar Maulana Shehu Ibrahim Niasse, duk da haka bai taba da’awar mallakar wannan ɗariƙar ba balle har ya kira kansa a matsayin Shehin da ya ke sanyawa ko kuma hanawa a karan kansa sai dai kawai yana yin nuni ne da abin da fikihun wannan ɗariƙar ya tanadar.

     

    Sheikh Abdulbaƙi Miftah, a cikin littafinsa mai suna واء على الشيخ أحمد التجاني وأتباعه”, ” a babi na biyar wanda ya ƙunshi bayanin irin yanda almajiran Shehu Tijjani, da kuma magadansa su kai ƙoƙari wajen yaɗa wannan ɗariƙar tamu.

     

    Marubucin ya yi ƙoƙarin fitar da kididigar mutanen da suka karbi ɗariƙar Tijjaniyya, daga hannun manyan manyan Halifofin Shehu Tijjaniyya ya kuma bayyana cewa Shehu Ibrahim Niase shi ne ya fi kowa girma, a yaɗa ɗariƙar domin ta hanyarsa sama da mutane miliyan 30 ne suka karɓi ɗariƙar kai tsaye.

     

    Duk da irin wadannan nasarori, da Shehu ya samu amman a lokuta da dama yana cewa Shehunai na guda biyu ne akwai na zahiri da kuma na ɓoye Shehunan zahiri su ne Alkur’ani da kuma Sunnar shugaba Sallallahu alaihi Wa sallama, wanda kuma mun san babu wanda ya fi Shehu fahimtar su Shehinsa kuma na ɓoye yana cewa shi ne Maulana Shehu Tijjani, wanda yake tare da shi a ko da yaushe.

     

    Shi sanya ma da Sheikh Ahmad Sukairij da ya zo yabon Shehun ya ke cewa cewa…

     

    وإني أرى الشيخ التجاني خـاتـمـا

    وأنت الذي قد صرت في الخاتم الفصا

     

    Ka sani ya kai ɗan’uwana muridi ɗariƙar ba ta kowa ba ce wanda idan ya kore ka shi kenan ka koru ɗariƙar ta Shehu Tijjani ce duk wani Shehi wakili ne idan ka ga Shehin da kake tare da shi ya gaza ta fuskar sauke nauyin wakilci saboda

    Dalili wanda ya bayyana kana damar canja shi kuma babu abin da zai faru da kai domin ba bautarwa ba ce bawa da mai shi kowa daga kogi Shehu Tijjani yake sha.

    Share
  • Karanta Alqur’ani Yafi Karanta Salatul Fatih, Wannan Maganar Na Rubuce A Cikin Littafin Jawahirul Ma’ani

    Karanta Alqur’ani Yafi Karanta Salatul Fatih, Wannan Maganar Na Rubuce A Cikin Littafin Jawahirul Ma’ani

     

    …..Cewar Sheikh Sani Khalifa Abdulkadir Zariya

     

    Babu wani dan tijjaniyyan da yarda cewa Salatul Fatih tafi Alqur’ani, domin Shehu Tijjani da almajirasa basu fadi haka ba, kuma a littafin Jawahirul Ma’ani cewa aka yi karatun Alqur’ani yafi wuridin tijjaniyya da kowace irin wuridi idan mai karanta ta ya kiyaye haddodin ta. Shiyasa mu ‘yan tijjaniyya ba mu da wani littafin da muka rike fiye da Alqur’ani, kuma mu ‘yan tijjaniyya munfi kowa yawan mahaddata Alqur’ani musamman a nan Najeriya.

     

    Masu cewa ‘yan darika sunce Salatul Faith tafi Alqur’ani shashashai ne, makaryata ne, masharranta ne, ba wani abu yasa suke fadan haka ba illa yunkurin dusashe hasken tijjaniyya a wajen wawaye, amma hakansu bata cimma ruwa ba saboda Allah yana cewa :

     

    يريدون أن يطفئوا نور الله بأفواههم ويأبى الله إلا أن يتم نوره،

     

    ~ Sheikh Sani Khalifa Abdulkadir Zaria

    Share
  • Sheikh Ahmadu Tijjani Bai Lamunci Shan Taba Ba, Yaushe Wani Zai Zuƙi Wiwi Yace Shi Almajirinsa Ne

    Shehin da bai lamunci shan taba ba yaushe wani zai zuƙi wiwi ya ce shi almajirinsa ne

     

    Shehin Da Ya Zaɓi Ibada Da Nema Ilimi Fiye Da Sunnar Aure Yaushe Almajirinsa Zai Yi Zina.

     

    Shehin Da Ya Haddace Alqur’ani Yana Ɗan Shekara Bakwai Kuma Ya Faɗa Duniya Ya Nemi Sauran Illimmai Tun Da Kuruciyarsa Yaushe Ne Almajirinsa Zai Ce Ya Gama Neman Ilimi.

     

    Shehin Da Baya Sallah Sai Cikin Jam’i Akan Lokaci Yaushe Almajirinsa Zai Ce An Dauke Masa Sallah.

     

    Shehin Da Ya Ce Maka Ka Bi Umarninsa Cikin Umanin Allah Da Ma’aiki Salawatullahi Wasalamuhu Alayhi In Ka Ga Ya Saɓa Ka Barshi Yaushe Almajirinsa Ya Koyi Wasa Da Hakkin Allah.

     

    Manufata Ka Gane Masu Shisshigi Da Barna Da Sunnan Yan Tijjaniyya Ko Alama Ba Su yi Tare Da Shehu Tijjani (RTA).

     

    Allah Ya Bamu Lafiya Da Zaman lafiya Albarkar Shehu Tijjani. Amiin

    Share
  • WANENE SHEIKH AHMAD TIJJANI ABUL ABBAS RA? TARIHINSA DA RAYUWARSA RTA.

    WANENE SHEIKH AHMAD TIJJANI ABUL ABBAS RA? TARIHINSA DA RAYUWARSA RTA

     

    1. NASABARSA RTA

     

    Shine Sheikh Ahmad dan Muhammad dan Mukhtar dan Ahmad dan Muhammad dan Salim dan Abil Idi dan Salim dan Ahmad (Alwaniy) dan Ahmad dan Aliyu dan Abdullah dan Abbas dan AbdulJabbar dan Idris dan Idris dan Is’haq dan Aliyu (Zainul Abidina) dan Ahmad dan Muhammad (Nafsuz Zakiyya) dan Abdullahil Kamil dan Alhasan Musannah dan Alhasan Alhasan Assibdiy dan Sayyidi FADIMA ‘yar Manzon Allah SAWW daga Imam Aliy, RA,

     

    A Wajen Mahaifiya Dan Sayyidi Aisha ne Diyar Abiy Abdullah Muhammad bn Sanusi Attijaniy Almadawiy An haife shi Aini Madiy 13, Safar 1150@H (15, June 1737) yau Shekaru (295)

     

    An Yi masa Aure da Shekaru 15, bayan Shekara daya Mahaifansa biyu sun yi Wafati Rana daya 1166, sai ya Saki Matarsa domin shiga Neman Mazaje Masana Allah don Neman yardarSa

     

    MALAMAN SHEIKH AHMAD TIJJANI RTA

     

    Ya Karanci Qur’ani Wajen Sheikh Abu Abdullah bin Hamwu Attijaniy ya rasu 1162@H ya haddace da Shekaru 7, bayan Kammalawa

     

    Ya cigaba da Neman Ilmoman Shari’a na Tushe da na Rassa har yazama Cikakken Malamin da zai iya koyarwa da yin Fatwa da Shekaru 21

     

    SAURAN SHEIKHANAI DA YA KARBI ILMOMA, ASRARAI, AZKARAI DA AURADAI WAJEN SU DA SHEKARUN WAFATINSU RTA

     

    Sheikh Sayyidi Abu Dayyib bn Muhd 1180

    Sheikh Ahmad As Saqaliy Fass 1177

    Sheikh Sayyidi Muhd Hasan Alwanjaliy 1185

    Sheikh Abdullah bin Sayyidi Arabiy 1188

    Sheikh Abul.Abbas Ahmad Dawwash Tazi 1204

    Sheikh Sayyidi Abdulkadir bn Muhd

    Sheikh Muhd bn Abdullahi Attaziy

    Sheikh Mahmudul Alkurdiy Al Iraqiy 1195

    Sheikh Ahmad bn Abdullahi Alhindiy 1187

    Sheikh Muhd bn Abdulkareem Assammaniy

    Sheikh Ahmad Alhabib Algumariy 1166

    Sheikh Muhd bn Abdurrahman Al Azhariy 1208

    Sheikh Al Arif Muhammad bn Fudail

     

    KADAN DAGA CIKIN DARIQUN DA YA KARBA:

     

    Dayyibiyya Jazuliyya As Shazaliyya

    Qadiriyya ya Karba a Fass

    Nasiriyya Ashazaliyya

    Algumariyya As Siddikiyya

    As Sheikhiyya As Shazaliyya

    Khalwatiyya

    Arrahamaniyya Alkhalwatiyya

    Alkhalwatiyya Wajen Sheikh M Alkurdiy RA

     

    KASASHE WASU GARURUWAN DA YA ZAUNA

     

    Kadan daga Kasashen da ya tafi ya ZAUNA don Neman Ilmoma da haduwa da Masana Allah :

     

    Ya fara da Mahifarsa Ainu Madiy, Fass Magrib, Baladul Abyad, Tsakiyar Kusancin Jaza’ir

    Tilmisana Zaman Ibada da Karantarwa

    Tunis, Masar kan Hanyar zuwansa Hajji

    Makkatul Mukarrama da Madinatu Munawwara

    Shallah, sai KASRU Abiy Samgoon sai Tuwat

    Karshen ya Koma da Fass Nan ya Yi Wafatinsa

     

    KWAREWARSA A FANNOMAN ILMI

     

    Ya Karanci dukkan Fannonan Ilmi na Sharia da Hakika (Sufanci) Kuma ya Kware a dukkansu MusammanTauhidi Tafsiri, Tajweedi, Hadisi da Sufanci Kuma ya karantar dasu sosai da gaske

    Sheikhani Zamaninsa sun masa Sheda tare da Sallama mashi

     

    FARA DARIKAR TIJJANIYYA A DUNIYA (249)

     

    Bayan Samun Al Fathul Akbar ya samu tashi Darika Mai Zaman Kanta daga Sayyidil Wujudi 1196 Mai Istigfari 100 da Salati 100 har zuwa 1200 aka cika masa da Haila 100

     

    Ya Hai Mukamin Kudbaniyatul Uzma a farkon Muharram 1214 an Kuma nadashi a Filin Arfa, bayan kwanaki 40, ya Hau Mukamin Khatmiyya da Katmiyya 18 Safar 1214@H

     

    AUREN SHEHU TIJJANI RA A KARO NA BIYU:

     

    Bayan ya cimma Muradinsa na samun yardar Allah ya sakeyin Aure don Koyi da Annabi saw, ya sayi Kuyangi biyu ya ‘yan tasu ya Aure su har sun Haifa masa ‘ya’ya guda biyu

     

    Yayi Wafati a Ranar Alkhamis 17Shawwal 1230

    Yanada Shekaru 80, ya bar Mata biyu Sayyida Mabruka da Sayyida Mubaraka da ‘Ya’ya biyu Sayyidi Muhammadul Kabeer da Sayyidi Muhd Alhaeeb an rufe shi a Zawiyyar sa, Fass RTA yau kimanin Shekaru (215)

     

    Sheikh Imam Al Mufty Abu Abdullahi Muhd bn Ibrahim Addakkaliy ya masa Sallah tare dukkan Mutanen Kirki Dake Kasar Algeria.

     

    Ya bar Manyan Waliayai da Manyan Sharifai da Manyan Sheikhunan a Matsayin Khalifofansa. Masha’Allah

     

    Abdulhakeem Ahmad Ya’akub Gusau 30/08/23

    13/Safar/1445 @H HAPPY MAULIDIL KHATMI.

    Share
  • BIDIYO; Jawabin Sheikh Dahiru Bauchi RA Akan Falalar Wuridin Darikar Tijjaniyya.

    Jawabin shahararren malamin addinin Musulunci kuma babban shehin Ɗarikar Tijjaniyya na duniya Sheikh Dahiru Usman Bauchi RA.

     

    Babban Malami Wanda yake gabatar da Tafsirin Alkur’ani mai girma a jihar Kaduna ya bayyana falalar wuridin Darikar Tijjaniyya inda yayi kira ga daukacin al’ummar musulmi rasu shiga Darikar Tijjaniyya don samun falala a duniya da lahira.

     

     

     

     

    Muna rokon Allah ya saka wa MAULANA Sheikh Dahiru Bauchi RA lafiya da nisan kwana albarkacin Annabi Muhammadu ﷺ. Amiiiin

     

    Tijjaniyya Media News

    Share
Back to top button