FADAKARWA

  • Sheik Ibrahim Inyass yace; Amma ni bazan taba ganin Musulmi Mai sunan Manzon Allah SAW ba (wato Amadou Lamine-Guèye) na kyaleshi na zabi Kafiri ba,

    SIYASA DA TARIQA

     

    A 1960 lokacin da aka fara Siyasa A senegal Léopold Sédar Senghor Ya fito yana neman Shugabancin Qasa, Shima lokacin Amadou Lamine-Guèye Ya fito yana Neman Shugabancin Qasar.

     

    Kamar yadda Al’adar Siyasa take kowa Ya ringa tallata dan Takararsa kuma koya yakeso yace ra’ayinsa daya yake Dana Sheikh Ibrahim Niasse RTA, Har Abun yaso ya zama Rigima tsakanin Muridai.

     

    Da Sheikhu RTA Yaji Labari sai yasa aka Tara Muridai a masallaci sannan yace musu naji rikici yana so ya balle tsakaninku, Tsakanin wanda suke son Senghor da Lamine kowa yana danganta dan takararsa dani Toh ina so na gayamuku Abunda yake Tsakanina daku shine wannan (Sai Sheikhu Ya ’Daga Carbinsa Sama ya nuna musu). Ma’ana Tariqa ce kawai tsakanina daku.

     

    Sheikhu ya cigaba da cewa “Amma ni bazan taba ganin Musulmi Mai sunan Manzon Allah SAW ba (wato Amadou Lamine-Guèye) na kyaleshi na zabi Kafiri ba, Amma duk da haka Ban hana kowa ya zabi wanda yake so ba.”

    Naji wannan Qissar wajen Sheikha Bilqees Niasse RTAnha 2015

     

    ABUN LURA

    1-Wannan yana nuna mana Shehi bashi da iko ya takurawa Muridi wani dan takara.

    2-Haka zalika zamu fahimci cewa tariqa daban siyasa daban.

    3-Kamar yadda zamu fahimci wajibin Shehunnai ne su fito su hana muridai samun sabanin tsakaninsu.

     

    Daga: Aliyu Uthman Bashir.

    Share
  • Banbancin Masu Shirya Tarukan Walimar Siyasa Da Tarukan Mauludi

    KU SUFAYE KU GODEWA ALLAH.

     

    Idan ka dauki dubban kudade ka baiwa biri, da kwayar Ayaba guda, mai yiwuwa sai ya yayyage wadannan kudaden, ya dauki Ayaba guda, alhali wadannan kudaden zasu sayi dubban Ayaba da zai dauki lokaci yana mora.

     

    To amma kai da kasan amfanin Kudaden, kaga idanunka basu ma zuwa kan wannan Ayabar guda, balle ka shagala da ita.

     

    To haka abin yake ga wadanda suka fahimci girman MANZON ALLAH (S.A.W) suke Shirya tarukan Mauludinsa, da wadanda suka fahimci girman wasu ababen Duniya suke shirya tarukan nuna murna akansu, ta hanyar kyarar yi ga MANZON ALLAH (S.A.W).

     

    Yadda bazaka iya ganar da Birrai gane Muhimmancin kudaden nan sama da Ayaba guda ba, haka zalika suma wadannan bazaka iya ganar dasu Muhimmancin nuna soyayyar MANZON ALLAH (S.A.W) da godewa ALLAH a wannan Janabi sama da wanin hakan ba.

     

    Face dai yadda wadannan Birran zasu yayyaga wadannan kudaden, suma haka zasuke yayyaga muku mutunci saboda nuna soyayyarku ga madaukakin da babu kamarsa.

     

    KU GODE ALLAH DA ALLAH YA ZABE KU YA FAHINTAR DA KU GANE GIRMAN WANDA YAKE GIRMAMAWA, KUMA KU ROKAR MUSU ALLAH SUMA YA GANAR DA SU GANE HAKAN. AMIIIIN YAA ALLAH.

     

    Daga: Muhammad Usman Gashua

    Share
  • Sheikh Ibrahim Maqari Ya Bayyana Matsayar Sa Bayan Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa 2023 A Najeriya.

    DALILAN DA SUKA HAIFAR DA WANNAN TUNANIN (A FAHIMTATA).

     

    1- Zamowarsa Limami a babban Masallacin kasa, hakkinsane ya zamo mai yin kira akan duk abinda zai tabbatar da dorewar Nigeria a matsayin kasa daya, al’umma daya, daga barin duk abinda zai haifar da wariya, tsangwama ko kuma cin fuskar ga wasu al’umma, ta hanyar aje dukkan banbance-banbance.

     

    2- Wannan dalilin yasanya yayi iya kokarinsa matuka cikin karatuttukansa yana mai kira akan a kasa irin ta Nigeria da take Secular State, a zabi chanchanta daga barin duba bambancin Addini, Jam’iyya ko kuma bangaranci, shine Malami guda cikin Malamai da na sani wanda bai dauki bangare ba a siyasa baldai yana nun ko da Kristane yafi Musulmi chanchanta, to a zabi Kristan ta hanyar barin Musulmin.

     

    3- Ko da yake wasu bangaren Yan Siyasa, sun shigo da Addini cikin harkalarsu, ta hanyar Muslim-Muslim Ticket, a lokacin da ake ganin idan Musulmi ya fito daga Arewa, to Mataimakinsa zai zamo wanda ba Musulmi ba daga kudu a bisa ga Al’ada, sai aka samu wasu daga Maluman Addini suka fito karara suka nuna kyamar Kristoci a zahiri, mai yiwuwa su kuma sai hakan ya basu haske akan cewa bara suma su hade wuri guda su zabi nasu.

     

    4- Kaga kenan hakan darasine ga Maulana Prof. Ibrahim Maqari da yake ta kira akan Tolerance, a nesanci bangaranci, ya fahimci cewa “wadanda yake yi dominsu duk basu duba hakan face su kawai na su suka sani, kuma shi suka sanya a gaba”.

     

    A KARSHE DAI SHIMA MAI YIWUWA YANA GAB DA SAUYA MATSAYA ZUWA GA KIRA GA A ZABI MUSULMI MAI NAGARTAR HALAYE A ZABUKA MASU ZUWA.

     

    ALLAH SHI KYAUTA. AMIIN YAA ALLAH

     

    Daga: Muhammad Usman Gashua

    Share
  • Jawabin Sheikh Dahiru Usman Bauchi RA A Zaben Shugaban Kasa Shekara Ta 2023.

    HIKIMOMINE CIKIN FATAWOWIN GUDA BIYU, MADALLAH DA WANNAN JAGORA GWANIN ZAYYANA ADALCI A KALAMANSA.

     

     

    Na lura dayawa wasu daga yan uwa sun shiga rudani, bayan sauraron zantukan sauti guda 2 daga Maulana Sheikh (R.T.A) game da matsayarsa akan wannan zabe, inda wasu suke ganin, kamar zancen farko na sabawa na biyunsa, da dai wasu al’amura makamanta haka.

     

    A iya dan karanin nazari na, Ni banga abin daure kai ba cikin fatawowin Maulana Sheikh game da wannan zabe ba, domin bita daya nayiwa zancen na fahimceshi tarwai, ba tare da na sake bita ba.

     

    1- Fatawa ta farko Maulana (R.T.A) yayitane ga Mujtama’a Duniyar (Tijjanawa) masoya akan kowa yaje ya zabi wanda ya kwanta masa a rai daga cikin yan takarkaru (Ko da Dan Jarida ya same shi), wannan fatawace da Maulana Sheikh ya sauke hakkin dake wuyansa a matsayinsa na uba kuma daya daga cikin jagororin Tijjanawa a Dunuya, kasancewarsa mai yawan hikima kuma ma’abocin adalci, sai ya baiwa kowa dama, tunda wannan sha’anine na Duniyarsu. Misali, kamar dai layin wayar Salulane da zaka tambayi Maulana Sheikh da wanne ya dace kayi amfani tsakanin MTN, AIRTEL, ko GLO, to zaice dakai kaje kayi amfani da wanda ya kwanta maka a rai, to haka suma yan takarar dake dukkan jam’iyyu.

     

    2- Fatawa ta biyu kuma da zamu lura Maulana Sheikh yayi amfani da kalma Muqayyada, wato makusanta wasu (Daga Family) sun sameshi da wanda suke so su zaba wanda shine Atiku, (Kasancewar su masu matukar ladabi da biyayya gareshi, basu son aikata abinda babu umarninsa ciki wanda hakan shine dalilinsu na zuwa gareshi) shi kuma a matsayinsa na uba mai yawan adalci da sakarwa kowa mara akan abinda babu sabon ALLAH cikinsa, sai yace da su shikenan suje su zabi Atikun harma domin kara girmamasu saboda hikima sai yayi amfani da kalma “gamayya” mu Wato dai Misali kamar suce sunason Amfani da layin MTN daga barin waninsa, kaga bazaice musu a’a ba.

     

    Sam-sam a fahintata zancen Maulana Sheikh na farko bai sabawa na biyu ba, sannan kuma zancen karshen bai kore na farkon domin baice kada a zabi wani dan takara sabanin Atiku ba, baldai kowanne da nasa matsayin gwargwadon wadanda akayi zuwa garesu, kuma wannan dama shine cika ta kamala irin na bayin ALLAH suna zance da kowa gwargwadon matsayi da kusancin dake tsakaninsu.

     

    YA ALLAH A KARA KULAWA DA SHA’ANIN WANNAN WALIYIN, A KARA MASA JURIYA DA HAKURI DA LAMARIN YAN ZAMANI, A KARA TSARE MASA MUTUMCI ALFARMAR MANZON ALLAH (S.A.W). AMIIN YAA ALLAH.

     

    Daga: Muhammad Usman Gashua

    Share
  • SHEIKH MAQARI: Siffofin Shugaba Nagari A Cikin Al’umma

    Maulanmu Sheikh Farfesa Ibrahim Ahmad Maqari Hafizafullah Ya Bayyana Matsayar Sa Akan Zabe 2023,

     

     

    Sheikh Ibrahim Maqari Ya Bayyana Cewa Akwai Siffofin Shugaba Nagari Da Ya Kamata A Zaba A Cikin Al’umma.

     

    Muna Addu’an Allah Ya Bamu Shugaba Nagari Ya Bashi Ikon Gudanar Da Nauyin Da Aka Daura Masa. Amiin Yaa ALLAH

    Share
Back to top button