FAIDAH

  • Tsananin Bin Sunnar ANNABI (S.A.W) Da SHEHU IBRAHIM NIASSE(R.A) Iri Daya Ne.

    Misalin Tsananin Bin Sunnar ANNABI(S.A.W) Da SHEHU IBRAHIM NIASSE(R.A) Yake.

     

    Akwai Watarana Da Ya Umarci Babban Jikansa, IMAM HASSAN CISSE(R.A) Ya Ja Sallah, Da IMAM Ya Tashi Yin Sallah, Sai Duk Bayan Fatiha Ya Ɗebo/Tsinto Ayoyi Daga Wata Surah, Sai Ya Biya Yayi Ruku’u,

     

    Da Aka Idar Sai SHEHU(R.A) Ya Ce; Idan Zaka Ja Ni Sallah Daga Yau, Ka Min Irin Sallar ANNABI(S.A.W), Idan Ya Ɗauki Surah Sai Ya Dire Ta,

     

    Kada Ka Min Irin Sallar Mutan Gari Kaza, a Tsinto Ayoyi, Duk Da Hakan Ba Laifi Bane, Amma Yadda ANNABI Ya Yi Nake So a Min.

     

    ALLAH Ya Ƙarawa SHEHU Karama, Ya Bamu Albarkar Masu Albarka, Ameeen.

     

    (©️Sabo Ibrahim Hassan).

    Share
  • Sama Da Almajirai Miliyan 100 Ne Suka Sallamawa Sheikh Ibrahim Inyass. Inji Kungiyar Rabidatu Alamil Islami Dake Saudi Arabia.

    Sheikh Ibrahim Inyass Al Khaulaq RA Yana Da Almajirai Miliyan 100 Wanda Suka Sallama Masa A Africa.

     

    ……Inji Kungiyar Rabidatu Alamil Islami Dake Saudi Arabia.

     

    Binkice Ya Tabbatar Da Cewa Akwai Almajiran Sheikh Ibrahim Inyass RA Sama Da Miliyan 100 A Kasashen Afirka.

     

    Wanda Suka Sallamawa Shehin Malamin A Africa Kadai. Inji Kungiyar Rabidatu Alamil Islami Dake Saudi Arabia.

     

    ALLAH Ya Karawa SHEHU Ibrahim Masoya Da Kusanci Ga Fiyayyen Halitta ANNABIN Mu Muhammadu SAW. Amiin

     

    Daga: Babangida A Maina

    Share
  • JERIN SUNAYEN YA’YA’N MAULANMU SHEHU IBRAHIM INYASS MAZA DA MATA SU (75).

    JERIN SUNAYEN YA’YA’N MAULANMU SHEHU IBRAHIM INYASS MAZA DA MATA SU (75).

     

    MAZA (38)

     

    1. Shehu Abdullahi

    2. Shehu AbdurRaheem

    3. Shehu Abdulmalik

    4. Shehu Abdul’Ahad

    5. Shehu Ahmadu

    6. Shehu Muhammadu Mujtaba

    7. Shehu Abubakar

    8. Shehu Muhammadu Mansuru

    9. Shehu Muhammadu Naziru

    10. Shehu Muhammadu Mahi

     

    11. Shehu Muhammadu Hadi

    12. Shehu Muhammadu Aminu

    13. Shehu Muhammadu Makiyu

    14. Shehu Muhammadu Ma’amunu

    15. Shehu Muhammadu Akibu

    16. Shehu Muhammadu Muntaka

    17. Shehu Muhammadu Arabi

    18. Shehu Muhammadu Muktar

    19. Shehu Muhammadu Nasiru

    20. Shehu Muhammadu Mahdi

     

    21. Shehu Muhammadu Mujtaba

    22. Shehu Muhammadu Kurashiyu

    23. Shehu Muhammadu Shafi’u

    24. Shehu Muhammadu Mahmudu

    25. Shehu Muhammadu Halifa

    26. Shehu Muhammadu Yasin

    27. Shehu Muhammadu Tuhami

    28. Shehu Muhammadu Murtadha

    29. Shehu Muhammadu Munhaminna

    30. Shehu Muhammadu Siraja

     

    31. Shehu Muhammadul Amin

    32. Shehu Muhammadul Abdurahman

    33. Shehu Muhammadu Abdulkarim

    34. Shehu Muhammadu Sahibu kahiri

    35. Shehu Muhammadu Nurul dini

    36. Shehu Muhammadu Sahibul Makami

    37. Shehu Muhammadu Sahibul Judi

    38. Shehu Muhammadul Muntazir.

    .

    MATA (37)

    1. Sayyada Maryam

    2. Sayyada Maryam

    3. Sayyada Maryam

    4. SayyadaMaryam

    5. SayyadaHapsatu

    6. SayyadaUmamatu

    7. SayyadaUmamatu

    8. Sayyada Umamatu

    9. Sayyada Fadimatu

    10. Sayyada Fatimatu

     

    11. Sayyada Fadimatu

    12. Sayyada Ummu Kulsum

    13. Sayyada Ummul Khairi

    14. Sayyada Ummu Haniy

    15. Sayyada Ummu Habibata

    16. Sayyada Ummul Salmata

    17. Sayyada Ummu Salma

    18. Sayyada Aishatu

    19. Sayyada Aishatu

    20. Sayyada Nafisatu

     

    21. Sayyada Nafisatu

    22. Sayyada Nafisatu

    23. Sayyada Hafisatu

    24. Sayyada Rukayyatu

    25. Sayyada Rukayyatu

    26. Sayyada Rukayyatu

    27. Sayyada Khadijatu

    28. Sayyada Khadijatu

    29. Sayyada Hauwa’u

    30. Sayyada Rabi’atu

     

    31. Sayyada Barakatu

    32. Sayyada Lubabatu

    33. Sayyada Aminatu

    34. Sayyada Safiyatu

    35. Sayyada Saudatu

    36. Sayyada Rahmat

    37. Sayyada Zainabu

    .

    Allah Yabamu Albarkacin Su, Ya Azurtamu Da Zuri’a Daiyiba Ta Maulanmu Shehu R.t.a. Amiin

     

    Muhammad Izzuddin Abubakar

    Shehu Manzo Media Team

    Share
  • Musulman Najeriya Yan Tijaniyya sune mafiya rinjaye sama da mutum Miliyan 50 mabiya Darikan Tijaniyya a Najeriya.

    KUNDIN TARIHIN TIJANIYYA

     

    TAKAITACEN TARIHIN SHIGOWAN DARIKAR TIJJANIYYA A NIJERIYA

     

    Tarihin yaduwar Tijjaniyya a Nijeriya yana komawa ga mutane uku wadanda suka dauki dawainiyar yada darikar. Wadan nan mutane su ne, Shaihu Maulud Fal, Shaihu Umar Alfuti da Shehu Sharif Muhammad wanda aka fi sani da lakabin Sharu Zangina.

     

    • Shaihu Maulud Fal ya kasance daga cikin manyan ‘yan Tijjaniyya wadanda suka yi aiki sosai wajen yada darikar, musamman a arewaci da yammacin Afirka. Shi mutumin Muritaniya ne, amma ya yi tafiye-tafiye da dama. Ya wuce ta Kasar Hausa a kan hanyarsa ta zuwa aikin Hajji inda ya shigar da Modibbo Ahmadu Raje cikin darikar. Ahmadu Raje shi ne kakan galadiman Adamawa Muhammadu, kuma ijazar (takardar izinin shiga darikar) da Shaihu Fal ya rubuta masa da hannunsa har yau tana nan a adane a wurin zuri’ar Galadiman Adamawa.

     

    •Shehu Umar Alfuti babban dan Tijjaniyya ne wanda a sakamakon kokarinsa darikar ta samu kafuwa a dukkan sassan Afrika ta yamma. Umar Alfuti ya karbi darikar daga hannun Shaihu Abdulkarim Nakil wanda shi kuma tun da farko ya karbo ta daga Shaihu Maulud Fal, wanda muka gabatar da ambatonsa. Umar Alfuti ya zo kasar nan a zamanin Sarkin Musulmi Muahmmad Bello dan Shehu. Ya zauna a Sakkwato na wani lokaci, ya auri diyar Sarkin Musulmi Bello, sa’an nan ya wuce zuwa Makka inda ya game da shugaban Tijjaniyya na wannan zamani, Shaihu Muhammad Gali, wanda ya nada shi mukaddami a darikar. A kan hanyarsa ta komowa daga Hajji, Umar Alfuti ya biyo ta garuruwan Kukawa, Bauchi, Zaria, Katsina da Kano. A ko wane gari ya sauka, ya kan yi kokari ya nema wa darikar magoya baya. Bayan rasuwar Sarkin Musulmi Muhammad Bello, Umar Alfuti ya koma garinsu, Futa Toro, wanda a yau yake cikin kasar Senegal.

     

    • Shi kuwa Shaihu Zangina, wanda ake jin cewa yana daga cikin jikokin Shaihu Tijjani, ya kawo ziyara ne birnin Kano a zamanin Sarki Alu Maisango. Daga Kano ya wuce zuwa Zaria, kuma ya zarce har zuwa garin Lokoja a inda Allah ya yi masa rasuwa.

     

    Banda wadan nan Shaihinnai uku, akwai mutane da dama wadanda suka zo kasar nan don aikin yada darikar Tijjaniyya kamar su Shaihu Muhammad binu Usman wanda ya zo daga Moroko, da Shaihu Abdulwahhab wanda aka fi sani da lakabin ‘Sharif Ujudud’. Sai dai a cikin dukkan wadan nan Shaihinnai tasirin Sharu Zangina shi ya fi karfi; domin daga wajensa ne Shaihin da ya yada Tijjaniyya a yawancin biranen arewacin Nijeriya, watau Shaihu Muhammad Salga, ya karbi darikar. Daga cikin wadanda suka karbi darikar a hannun Shaihu Muhammadu Salga akwai Malam Ahmadu daga Gwandu, Malam Dangoggo daga Sakkwato, Malam Hassan Kafunga daga Kano, Malam Abba daga Damagaran, Malam Hassan daga Kwantagora, Malam Ibrahim Mai Rigar Fata daga Borno, da sauransu.

     

    Bayan tsawon lokaci da yaduwan Darikan Tijaniyya a Arewacin Najeriya sai daga bisani Dariqar ta shiga kudancin Najeriya ta hannun Muhammad Wali, mutumin Ilorin. Daga bayan shi ne Alfa Salih Abdulkadir ya kai dariqar Tijjaniyya Ibadan, lokacin da ya je Ilorin.

     

    Dariqar Tijjaniyya ta samu a Ijebu+Ode (Ogun State) a karni na Ashirin (20) ta hanyar ‘yan uwa kamar: Imam Hassan Amokeoja (D. 1920) da Alfa Alawaiye (D 1928).

     

    A yanzu haka a cikin Musulman Najeriya mabiya Darikan Tijaniyya sune mafiya rinjaye domin a kalla za’a iya samun sama da mutum Miliyan 50 mabiya Darikan Tijaniyya a Najeriya.

     

    Insha Allahu a karkashin wannan maudu’i na Kundin Tarihin Tijaniyya zamu rinka Kawo muku Tarihin Shehunnan Tijaniyya da irin gudunmawa da suka bawa Musulunci da Darika da Faidha baki daya, sai a ci gaba da binmu.

     

    A karshe muna rokon Allah ya sakawa Shehunnan mu da Alkhairi wadanda sukayi dawainiyar yada wannan Alkhairi har ya zo gare mu. Amiin Yaa ALLAH

    Share
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Ibrahim Inyass RA Ya Cika Shekaru 47 Da Rasuwa.

    TARIHIN SHEIKH IBRAHIM INYASS RA.

     

    ….Babban Malamin Musulunci Sheikh Ibrahim Inyass RA Ya Cika Shekaru 47 Da Rasuwa.

     

    Sheikh Ibrahim Inyass Al Khaulaq an haife shi a ranar (26/07/1900) a kasar Senegal, mahaifin sa Alhaji Abdullahi Tijjani, Sheikh Ibrahim ya kasance shugaba kuma jagoran sufanci da darikar Tijjaniyya a Senegal da yammacin Africa.

     

    Ya tashi bisa kularwar mahaifinsa, ya haddace Alkur’ani mai girma a hannun mahaifinsa A cikin kananan shekaru Yafa wallafa littafi yana da shekaru 21 a duniya.

     

    Sheikh Ibrahim Inyass yana da mabiya masu dumbin yawa a duniya, mabiya darikar Tijjaniya ya kasance mutun mai muhimmancin a cikin rayuwar mabiyan sa wurin koyi da halayensa da dabi’unsa a cikin rayuwar su. Anyi masa shaida da soyayyan Annabi ﷺ. Da kuma riko da sunnar Manzon Allah SAW.

     

    Sheikh Ibrahim Inyass shi ne dan Afirka ta Yamma na farko da ya jagoranci sallar a babban Masallacin Al-Azhar a Masar , bayan da aka yi masa lakabi da “Sheikh al-Islam”. Kuma malami na farko da Sarki Faisal na Saudiyya ya ziyarta a kauyen sa (Kaolack) a Senegal.

     

    Sheikh Ibrahim Inyass mutumin Afirka ne, ya kasance dan gwagwarmayar neman ƴanci a Afirka ta Yamma, saboda gudummawar da ya bayar don samun’ Ƴanci a Ƙasashen Afirka. Ya kasance aboki kuma mai ba da shawara ga Shugaban Ghana na farko, Kwame Nkrumah, da aboko Ga Gamal Abdel Nasser da Sarki Faisal na Saudi Arabia. Kuma Sheikh Ibrahim kasance Mataimakin Shugaban Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya tare da Faisal a matsayin Shugaba.

     

    A shekarar 1937 lokacin da suka haɗu da Shaykh Ibrahim a lokacin aikin Hajj a Makkah, Sarkin Kano, A Najeriya, Alhaji ‘Abdullahi Bayero ya yi mubaya’a ga shehin kuma ya bayyana kansa a matsayin almajirin Sheikh Ibrahim. Wannan lamarin ya sa Sheikh Ibrahim ya sami amincewar da yawa daga fitattun shugabannin Tijānīyyah A Arewacin Najeriya da ma wasu da dama wadanda ba Yan Darikar ba.

     

    Alhaji Abdulmalik Atta basarake ne daga Okene kuma Babban Kwamishina na farko a Najeriya A Kasar Ingila, yana daya daga cikin manyan almajiran Sheikh Ibrahim da kuma surukin shehin ta hanyar ‘yarsa Sayyida Bilkisu. Shaykh Ibrahim ya zama sanannen kuma jagoran darikun sufaye) a ko’ina cikin yankunan Kasar Hausa na Yammacin Afirka. Yana da miliyoyin Almajirai a duniya, yayi rubuce-rubuce da dama kusan sama da 75 a rayuwar sa.

     

    Sanadiyar Shehu Ibrahim Inyass RTA Ne Gwamnatin Najeriya Ta Sanya Hutun Maulidi Ya Zamo Doka A Kasa, Bayan Shehu Ya Zo Taya Najeriya Murnan Samun ‘Yanci A Shekarar lokacin ya gana da Firar minista na farko, Sir Abubakar Tafawa Balewa, sai Shehu ya bashi shawara cewa tunda kai Musulmi ne, ya kamata ka sanya ranar Maulidi ya zamo ranar hutu a Najeriya.

     

    Sheikh Ibrahim Inyass mabiyin addinin Islama, Mazhabar Maliki, Akida Ash’ariyya, Darikar Tijjaniyya. Sheikh Ibrahim Inyass ya rasu ranar 26 Yuli 1975 (shekaru 74) a wani asibitin St Thomas’ Hospital, London, dake kasar United Kingdom. Ya rasu yabar maza da mata da yawa da dama da kuma almajirai a sassan duniya da mabiya masa da miliyan 50.

     

    Allah ya jikan sa da rahma ya gafarta masa ya jaddada rahma a gare shi Albarkacin Annabi Muhammadu Sallallahu Alaili Wasallam. Amiin

     

    Rubutawa Da Tattarawa;

    Babangida Alhaji Maina (Tijjaniyya Media News

    25/07/2023 – 7/Muharram/1445.

    Share
Back to top button