KISSA

  • Wani Dattijo Ne Jikokin Sa Suka Ce Sunan So Ya Basu Labarin Wanda Yafi Kowa Jarumta a Cikin Al’umma

    LABARIN WALIYYI ABJADU

     

     

    Wani dattijo ne jikokin sa suka ce suna so ya basu labarin wanda yafi kowa jarumta a cikin al’umma, kuma wanda jarumtar sa ta amfanar dashi da musulmi a duniya da lahira, shine ya basu labarin WALIYYI ABJADU.

     

    Tsohon yace, A wata qasa daga qasashen duniya mai suna DAURUL FALAK, an haifi wani kyakkyawan yaro a ranar da rana ta fito bayan hasken wata ya kau, cikin wata daga watannin arabiya wanda tayi daidai da shekara a shekarun miladiyya. Sunan mahaifin yaron KAUKAB, sunan mahaifiyar sa BURUJ.

     

    Wannan yaron tun tasowar sa har yakai shekaru 18, bashi da aiki sai wayannan abubuwan:

     

    1. Tsantsar tauhidi, kiyaye sallar Farilla sau biyar a jam’i da azumin watan ramadana.

     

    2. Karatun kur’ani daidai gwargwado da neman ilimi.

     

    3. Koyi da sunnonin Annabi SAW da kuma kokarin biyayya ga iyaye bisa umurni da hani.

     

    Mutanen garin suna qaunar sa sosai har suke masa laqabi da ABJADUL ISLAM. Bayan ya shekara 18 sai yayi mafarki da wani balarabe, yace masa sunana BADDU (بط) ina so ka shiga duniya domin neman yardar Allah ta hanyar koyi da bayin sa waliyai.

     

    Yana farkawa ya nemi iznin iyayen sa ya shiga duniya, sai yaje wata qasa a qasashen yamma, ya gamu da wani waliyyi ana kiran sa KHATMUT TIJJANI. Ya nemi iznin zama dashi sai yace masa “maraba da zuwa Abjadu, ai nasan da zuwan ka, toh ni dai bani komai sai abubuwa guda uku, amma duk wanda ya riqe su sai ya shiga aljanna ko baya so, sune”:

     

    1. Istigfari 100, Salatil Fatihi 100, Hailala 100 bayan sallar asuba da na la’asar.

     

    2. Istigfari 30, Salatil Fatih 50, hailala 100, jauhara 12 sau daya a rana kullum.

     

    3. La ilaha illallah ba adadi ranar juma’a bayan sallar la’asar gabanin faduwar ranar har magariba.

     

    Wannan saurayin yace zai iya, waliyin nan yace toh naji amma akwai sharadi, dole ka daina neman madadin wani waliyyi in ba ni ba, ba zaka hada wannan wuridin da wuridin wasu waliyai ba, ba zaka daina yin wannan wuridin ba har mutuwa, saurayi yace da himmar ka maulana an gama. Waliyin nan yace to daga yau sunan ka ABJADUL IMAN.

     

    Haka saurayin nan yayi ta kokarin kiyaye wuridin nan daidai gwargwado har ya shekara 40, a lokacin sai khatmut Tijjani yace masa yanzu ka kai muqamin da zan turaka wurin babban da na, in kaje zai maka aure bayan ka tsallake ayyukan da zai saka ka.

     

    Kwanci-tashi sai ABJADUL IMAN ya isa garin da khatmut Tijjani ya labarta masa amma sai an tsallake wani teku ake isa garin. A bakin tekun an rubuta SUNAN WANNAN TEKUN FAIDA, TAKA DA QAFARKA KA WUCE IN AN MAKA IZNIN ZUWA. Ai kuwa Abjadu sai ya fara taka ruwan nan bai nitse ba, amma yana zaton zai dade bai kai tsakiyar ruwan ba, sai yaga taku 7 ya kaishi garin dake tsakiyar ruwan, an rubuta BARKA DA ZUWA GONAR ARUFAI.

     

    Bayan ya shiga sai ya ga jama’a kowa ya shagala da kanshi, babu mai magana da wani, Yana isa fadar garin sai ya shiga ya miqa takarda, aka kaishi wurin Sarki wanda shine babban yaron khatmut Tijjani. Yayi masa maraba sannan yace masa, zan maka aure amma sai ka tabbatar min da cewa za ka iya riqe mata. Shiga ga daki can ka dinga karanta abinda ka gani a jikin bangon dakin har sai ka fahimci yadda ake noma ba tareda fartanya ko galma ba, da yadda ake mutuwa ba tareda an daina numfashi ba.

     

    Bayan dan lokaci, Abjadu ya zo gun sarki da amsoshi gamsassu, sarki yace lallai yanzu kam ka cancanci aure, zan aura maka mata biyu a lokaci daya, kuma sunan ka ya zama ABJADUL ISHAN daga yau. Saurayi yayi godiya, aka daura masa aure da mace biyu, ta farko sunan ta BARA’ATU, ta biyu sunan ta FANAITU.

     

    Alhamdulillah! Yara kunji labarin waliyyi Abjadu wanda yafi kowa jarumtaka da amfanuwa tareda amfanarwa. Iznin fita neman ilimin a farko Annabi yayi masa, na biyu Shehu Tijjani yayi masa, a qarshe kuma ya samu damanar Shehu Ibrahim akan FA ASGARU ATBA’IY BARI’UN MINASH-SHIRKI wato har abada ba zai yi shirka ba, kuma FA ASGARU ATBA’IY UNILU FANA’A wato ya samu qarewa cikin zatin Allah.

     

    Wannan labarin bushara ne ga dukkan batijjane, da iznin Annabi ka sadu da Shehu Tijjani, da iznin Shehu Tijjani ka sadu da shehu ibrahim, saduwa da Shehu ke tsallakar da mutum daga sharrin duniya amma in ka yi tarbiyatul azkar bayan zuciyar ta cika da sadiqar soyayya da hidima gareshi.

     

    Mu qara riqe abubuwan da muke kai, wallahi a yau mu Allah yake dubawa yake saukar da rahmar sa, fushin sa ga halittu kuma domin mu yake Afwa, mune nashi, mune masoyan shi, mune bayin sa na haqiqa.

     

    Allah kayi tsira da aminci ga Annabi Muhammad, ka ninka yardar ka ga katimul wulaya, ka cigaba da daukaka sunan sahibul faida.

     

    ✍ Sidi Sadauki.

    Share
  • KISSA; Haduwar Sheikh Ibrahim Inyass RA, Tare Da Likatan As Mr, Z.Y A London.

    ‘KISSA: Lokacin Da SHEHU IBRAHIM NIASSE (R.A) Ya Je Asibiti a London, Sai Likitansa Wai Shi, Mr. R.Y. Ya Zo Yayi Masa Allura Da Idan Har Aka Yiwa Mutum Zai Yi Bacci Ne Na Awanni Bakwai Alal Akalli,

     

    Bayan Fitar Likita Da Awanni Biyu Kacal Sai Ya Jiyo Karatun Al’Qur’ani a ‘Dakin SHEHU(R.A),

     

    Sai Ya Fara Yiwa Shehu Hassan Cisse (R.A) Fada Don Me Suka Bar Wani Ya Shiga ‘Dakin SHEHU Zai Hana Shi Bacci???

     

    Sai Suka Nufo ‘Dakin, Ga Mamakinsu SHEHU(R.A) Ne Yake Karatun Al’Qur’ani,

     

    Sai Likitan Ya Fara Fargabar Wani Abu Mummuna Na Iya Samun SHEHU Don Haka Ya Ce:

     

    Lallai SHEHU Ya Samu Ya Koma Yayi Bacci, Sai SHEHU(R.A) Ya Ce Da Imam Hassan Cisse (R.A):

     

    “Ka Gayawa Likita Cewa Ni Tunda Na Cika Shekaru 30 a Duniya Na Ga Awa 24 Sun Min ‘Kadan Na Yi Duk Ayyukan Da Nake So, Don Haka Na ‘Dorawa Kaina Cewa Baccin Awa Biyu Kawai Zan Riqa Yi a Kullum”.

     

    (Daga; Littafin Imam Nasir Adam Mai Suna:

     

    الشيخ إبراهيم إنياس الداعية العالمي.

     

    Shafi Na; 105).

     

    SHEHU(R.A) Kenan!!!

     

    Himma Bata Ire-Irenmu Ragwaye Ba!!!

     

    (©️Dr. Tahir Lawan Muaz Attijany ✍️)

     

    Barhama Kenan, Masani Na Rabbani!

     

    Ya ALLAH! Ka Barmu Da’iman Da Soyayyar Masoyan MANZONKA(S.A.W),

     

    Ya ALLAH Ka ‘Kara Nutsar Damu Cikin Ambaton MANZON ALLAH(S.A.W), Amiin

     

    Allahumma Ameeeeen.

    Share
  • Wata Rana Wani Balarabe (A Lokacin MANZON ALLAH(S.A.W) Yana Cikin Tafiya a Daji Bayan Ya Kamo.

    ‘KISSAR DAMO;

     

    Wata Rana Wani Balarabe (A Lokacin MANZON ALLAH(S.A.W) Yana Cikin Tafiya a Daji Bayan Ya Kamo Wani ‘Katon Damo Domin Ya Kai Gidansa Ayi Abinci Da Shi, Yana Cikin Tafiya Sai Ya Hangi Wani Taron Mutane.

     

    Ya Riski Mutanen Yana Tambayarsu Shin Me Yake Faruwa Ne???

     

    Sai Mutanen Suka Ce Da Shi: “Wai Muhammadu Ne ‘Dan Abdullahi Ya Zo Yana Cika Mana Baki Wai Shi Annabin ALLAH Ne”.

     

    Take Balaraben Nan Ya Samu Ya Kutsa Kansa Da Karfin Gaske Cikin Taro Ya Riski MA’AIKI(S.A.W) Inda Ya Ce Da Shi: “Ya MUHAMMADU! Ba Zan Yi Imani Da Kai a Matsayin Annabin ALLAH Ba Har Sai Wannan Damon Yayi Imani Da Kai”

     

    Nan Take Ya Jefa Wannan Damon Akan ‘Kafar SHUGABA(S.A.W) Cikin Hanzari Damon Ya Nemi Ya Gudu Daga Wajen Sai NABIYYUR-RAHMATI(S.A.W) Ya Yiwa Damon Nan Magana Inda Ya Ce Da Shi Ya Tsaya Kuma Ya Juyo Baya.

     

    Take Damon Ya Juyo Ga MA’AIKI(S.A.W) Ya Ce Da Shi:

     

    “Ina Jiran Umarninka Cikin Girmamawa Ya RASULULLAH!”.

     

    *.GA YADDA HIRARSU TA KASANCE:

     

    MANZON ALLAH(S.A.W): “Waye Kake Bautawa???”

     

    DAMO: “Ina Bautawa ALLAH Ne Wanda Buwayarsa Da MulkinSa Yake Ko Ina, Mamallakin Sammai Da ‘Kassai, Wanda Ya Sanya RahamarSa a Aljannah, AzabarSa Kuma a Wutar Jahannama”.

     

    MANZON ALLAH(S.A.W): “Waye NI Kuma???”

     

    DAMO: “Kai Ne MANZON ALLAH Ma Mallakin Sammai Da ‘Kassai, Kuma Cikamakon Annabawa, Amincin ALLAHU Su Tabbata a Gare Ka, Duk Wanda Ya So Ka Ya Tsira, Wanda Kuwa Ya ‘Kika Ya Halaka”.

     

    Balaraben Nan Yana Jin Hakan Kawai Sai Jikinsa Yayi Sanyi, Ya Ce; Baya Buqatar Wata Shaida Bayan Wannan Inda Take Ya Ce;

     

    Ya Shaida Babu Abin Bautawa Da Gaskiya Sai ALLAH Kuma ANNABI MUHAMMADU(S.A.W) BawanSa Ne Kuma ManzonSa Ne.

     

    Sai Kuma Ya ‘Kara Da Cewa:

     

    “Lokacin Da Na Tarar Da Kai a Farko, Na Rantse Babu Wani Halitta a Doron ‘Kasa Da Nafi Tsana KamarKa(S.A.W),

     

    Amman Yanzu Da Na Saurare Ka Wallahi Na Fi Sonka Fiye Da Idanuwana, Kunnuwa Na, Baba Na, Mama Ta, Da ‘Ya’yana”,

     

    ALLAH Ya ‘Kara Mana ‘Kaunar ‘DAHA (S.A.W), Ya ‘Kar6i Rayukanmu Da ‘KaunarSA (S.A.W). Amiiiin

    Share
  • KISSA: Lokacin Da ‘Yan’uwan ANNABI YUSUF (A.S) Suka Zo Wajen Mahaifinsu ANNABI YA’AQUB (A.S) Da Rigar Shi (Yusufa).

    ‘KISSA (Mai Ban Tausayi)

     

    A Lokacin Da ‘Yan’uwan ANNABI YUSUF (A.S) Suka Zo Wajen Mahaifinsu ANNABI YA’AQUB(A.S) Da Rigar Shi(Yusufa).

     

    Sai Ya Ce:”Kai Wannan Kura Da Tausayi Take, Ta Yadda Ta Cinye YUSUF Amma Bata Kekketa Rigar Shi Ba”.

     

    Sai Ya Fashe Da Kuka Mai Tsanani, Sai Mala’ika Jibrilu Ya Zo Wajen Shi(ANNABI YA’AQUB(A.S),

     

    Ya Ce Masa:”Ka Yi HAKURI Mai Kyau(HAKURI Wanda Babu Raki Babu Kuma Kai ‘Kara a Cikin Shi)”.

     

    Sai ANNABI YA’AQUB(A.S) Ya Runtse Idanuwansa, Kuma Ya ‘Boye Bakin Cikinsa a Cikin Ran Shi, Ya Ce:”HAKURI Mai Kyau”,

     

    Shikenan Sai ALLAH Ya Sakawa ANNABI YA’AQUB(A.S) Barci.

     

    Sai ALLAH(S.W.T) Ya Cewa Mala’ika Jibrilu:”Hakika YA’AQUB Ya Samu HAKURI Mai Kyau a Ran Shi”.

     

    Sai Mala’ika Jibrilu Ya Sauko Zuwa Gare Shi a Surar YUSUF, Lokacin Da ANNABI YA’AQUB(A.S) Ya Gan Shi,

     

    Sai Ya Fashe Da Kuka Ya Ce:”Ya Abin Da Rayuwa Take ‘Kauna!!!”.

     

    Sai Mala’ika Jibrilu Ya Farkar Da Shi, Ya Ce Masa:”Ina HAKURI Mai Kyau ‘Din???”

     

    Sai ANNABI YA’AQUB(A.S) Ya Damki ‘Kasa Ya Cika Bakin Shi Da Ita, Ya Ce: “ALLAH Na Tuba Zuwa Gare Ka”.

     

    Sai Mala’iku Suka Fashe Da Kuka(Saboda Tsananin Tausayin ANNABI YA’AQUB(A.S).

     

    Sai ALLAH Ya Cewa Mala’ika Jibrilu:

     

    “Ka Shaidawa ANNABI YA’AQUB(A.S) Ya Zubar Da ‘Kasar Dake Cikin Bakinsa, Hakika Na Gafarta Masa, Kuma Na Yi Izini a Gare Shi Ya Iya Yin Kuka, SAI DAI KA DA YA KAI KUKAN SHI ZUWA GA WANI NA”.

     

    Ya SALAAM😭😭

     

    Ya ALLAH Ka ‘Kara Ba Mu Hakuri Da Juriya a Cikin Dukkan JarrabawarKA, Ko Da Bai Kai SABRUN JAMEEL Ba, Ameeeeen

    Share
  • ‘KISSA; An Yi Wani Bawan ALLAH a Zamanin Can Baya Ya Kasance Yana Bautar ALLAH (S.W.T) Har Na Tsawon Shekaru 600, Acan Bayan Gari Shi Kadai.

    ‘KISSA; An Yi Wani Bawan ALLAH a Zamanin Can Baya Ya Kasance Yana Bautar ALLAH(S.W.T) Har Na Tsawon Shekaru 600, Acan Bayan Gari Shi Kadai,

     

    ALLAH Cikin Buwayarsa Ya Hore Masa Wata Idanuwar Ruwa Mai Gudana, Da Kuma Wata Itaciyar Inabi Wanda Kullum Zai Samu Guda ‘Daya Ya Ci Shi Ne Abincinsa.

     

    Bayan Da Ya Rasu Sai UBANGIJI Ya Ce:”Ku Shigar Da Shi Aljanna Saboda Falala Ta Da Rahamaniyya Ta”,

     

    Sai Wannan Bawan Ya Ce:”Ya UBANGIJI! Haba Saboda Aiki Na Dai Da Kuma Bautar Da Na Yi Maka Na Shekaru 600″,

     

    UBANGIJI(S.W.T) Ya Ce Masa:”Ai Bautan Da Ka Yi Mini Bai Kai Darajar Ni’ima ‘Daya Da Nayi Maka Ba,

     

    Na Kai Ka Daji Na Sanya ‘Korama Kana Amfana Da Ita, Bayan Cikin Gari Mutane Na Zaune Ban Basu Ruwa Ba,

     

    Na Baka Inabi Kullum Sai Ta Tsiro Maka Da ‘Dan Itaciya Ka Ci, Bayan a Al’ada Sai Shekara-Shekara Take Yin ‘Yaya,

     

    Na Baka Lafiyar Yin Bauta, Sannan Na Hana Shaid’an Zuwa Inda Kake, Don Zan Iya Barinsa Ya Sace Imaninka,

     

    Duk Wannan Ni’imar Baka Gani Ba Sai Aikinka, Mala’iku Ku Kama Shi Ku Jefa Shi a Wuta”,

     

    Sai Ya Ce:”Ya UBANGIJI Na TUBA Ka Sanya Ni Aljanna Don Rahamarka Da Falalarka”,

     

    ALLAH(S.W.T) Mai Rahama Da Jinkai Ya Ce:”Ku Kai Shi Aljanna Don Rahamata”.

     

    (SOURCE; Akhrajahu Mubarak Fi Masnadihi, Ibreez Min Qalami Abdul Azeez, Shafi Na 349).

     

    *. DARASI:

     

    Hikimar Wannan ‘Kissar Anan Shi Ne; Babu Wanda Zai Shiga Aljanna Sai Da Falala Da Rahamar UBANGIJI(S.W.T),

     

    Mutum Ya Zama Bawan ALLAH Tsantsa(Ba Lebura Ba), Ba Bawan Ibadarsa Ba, Ko Shekara Nawa Ka Yi Kana Ibada Idan Dai An Tsaya Hisabin Aikinka Ba Zaka Sha Ba, Ka Godewa ALLAH Da Ni’imomin Da Ya Baka Na Kasancewa Musulmi.

     

    ALLAH YA SA MU CIKA DA IMANI, KA YARDA DA MU DON RAHAMARKA BA DON HALIN MU BA YA ALLAH, AMEEEEN

    Share
Back to top button