KISSA

  • KISSA; Kissan Sahabin Manzon Allah Abu Huraira Da Annabi Muhammadu SAW.

    ALBARKACIN HANNAYEN ANNABI (S.A.W).

     

    SAYYIDUNA ABU-HURAIRA (RTA) YACE:

     

    “Watarana nazo wajen ANNABI (S.A.W) da wani dabino dan kadan, Sai nace Masa :

     

    “YA RASULALLAHI YI MIN ADDU’A MANA, KA ROQA MIN ALBARKA ACIKIN WANNAN DABINON NAWA” Sai ya kar’ba, ya sanya shi a tsakanin hannuwansa, sannan yayi addu’a.

     

    Sannan yace min: “KAR’BI, KA SANYA SHI ACIKIN JAKAR DA KAKE ZUBA GUZURINKA ACIKI. KUMA DUK LOKACIN DA ZAKA CI DABINON, KA SANYA HANNUNKA KA DEBO DAGA CIKIN JAKAR, AMMA KAR KA JUYE”.

     

    Sai nace “to”.

     

    “Wallahi Sai da na rika ciyar da mutane masu yawa, kuma ina yin sadaqah daga cikin wannan dabinon. Kullum aciki nake ci nake sha. Ban ta’ba rabuwa da wannan jakar ba. Duk inda zanje tana nan a kwuibi na.”

     

    Na ci-gaba da cin Wannan dabino (Babu yankewa, babu Qarewa), Har ANNABI (S.A.W) yayi wafati, Har Tsawon lokacin Khalifancin Sayyiduna Abubakar Da Sayyiduna Umar, da Sayyiduna Uthman. (Allah ya yarda dasu)”

     

    Yayin da Aka kashe Sayyiduna Uthman (R.A), Sai jakar ta Fadi daga Hannu-na.” (Tsawon SAMA DA SHEKARA ASHIRIN KENAN).

     

    “Shin kuna so in gaya muku ko buhu nawa na fitar naci daga cikin Wannan jaka?”

     

    “WALLAHI NA CI SAMA DA BUHU DARI BIYU”.

     

    AWATA RUWAYAR KUMA, ABU HURAIRA (R.T.A) Yace: “Watarana (awajen yaki) ANNABI (S.A.W) Yace min

     

    “KIRA MIN MUTUM GOMA”

     

    Sai naje na kira su, Suka ci, Suka ci sai da suka Qoshi, Sannan yace In Sake kiran wasu Mutum goma din, su ma suka ci, Suka ci sai da suka Qoshi. Da haka Sai da Gaba dayan rundunar Kowa yaci dabinon nan ya Qoshi, Amma Dabinon yana nan kamar yadda yake tun farko” (BAI RAGU BA).

     

    A WATA RUWAYAR KUMA YACE:

     

    “MUSIBU GUDA UKU NE SUKA TA’BA SAMU NA AMUSULUNCI WADANDA BABU KAMARSU:

     

    1. WAFATIN ANNABI (S.A.W).

    2. KISAN SAYYIDUNA UTHMANU.

    3. FADUWAR WANNAN JAKA”.

     

    • Hadisai ne ingantattu, aduba musnad na Imamu Ahmad bn Hambal, juzu’i na 2, shafi na 352.

     

    • Tirmidhy ma ya kawo shi acikin Manaqibu abu huraira.

     

    •Sannan Imamul Baihaqy ma ya kawo shi a cikin

     

    Dala’ilun Nubuwwah, Juzu’i na 6, Shafi na 110 zuwa na 111.

     

    Allah ya barmu da ANNABI S.A.W. AMEEEEN..

    Share
  • Professor Ibrahim Ahmad Maqari Hafizahullah Ya Bada Kissan Wani Sarki Haruna Rasheed.

    PROFESSOR IBRAHIM AHMAD MAQARI ZARIA A CIKIN TAFSIRIN SA YACE :-

     

    Daga Babangida A. Maina

     

    Watarana Sarki Haruna Rasheed, Ya Gayyaci Wani Malami Domin Yazo Yayi Masa Wa’azi, Ayayin Da Wannan Malami Yazo, Sai Yace Da Sarki Haruna Rasheed “Ni Wa’azina Mai Zafine,Fa”

     

    SAI SARKI HARUNA RASHEED, YACE DA WANNAN MALAMI “TO KARIKE WA’AZIN KA MAI ZAFI” BANA BUKATA.

     

    YA KARA DA CEWA ” Allah Ya Tura Wani Bawan Sa Wanda Yafika Daraja Zuwa Ga Bawan Da Yafini Zunubi Da Sabawa ALLAH, Amma Sai ALLAH Yace Idan Wannan Dan Aike Nasa Mai Daraja Yaje Zuwa Ga Wannan Bawa Ma’abocin Manyan Zunubai, To Ya Kirashi Da Zance Mai Tausasa Zuciya “Kaulan Layyilan ( Zance Mai Dadi).

     

    WATO DAI WANNAN SARKI, YAYIWA WANNAN MALAMI ISHARA NE DA TARIHIN ANNABI MUSA (as) DA FIR’AUNA, AYAYIN DA ALLAH YA AIKI ANNABI MUSA ZUWA GA FIR’AUNA SAI YACE DASHI “IDAN KAJE KA YI MASA ZANCE MAI KYAU” NA TAUSASAWA DA LADABI YAYIN KIRAN SA ZUWA GA ALLAH.

     

    ASHE KENAN GA DUK WANI MALAMI, KOMIN GIRMAN ZUNUBIN MAI ZUNUBI, IDAN AKAJE YI MASA KIRA TO ANAI MASA KIRANE TA HANYAR TAUSASA MURYA DA KUMA ZANCE MAI KYAU DA NASIHA

     

    KAMAR YADDA ALLAH YACE

     

    ﺍﺩْﻉُ ﺇِﻟَﻰٰ ﺳَﺒِﻴﻞِ ﺭَﺑِّﻚَ ﺑِﺎﻟْﺤِﻜْﻤَﺔِ ﻭَﺍﻟْﻤَﻮْﻋِﻈَﺔِ ﺍﻟْﺤَﺴَﻨَﺔِ ۖ ﻭَﺟَﺎﺩِﻟْﻬُﻢْ ﺑِﺎﻟَّﺘِﻲ ﻫِﻲَ ﺃَﺣْﺴَﻦُ ۚ ﺇِﻥَّ ﺭَﺑَّﻚَ ﻫُﻮَ ﺃَﻋْﻠَﻢُ ﺑِﻤَﻦْ ﺿَﻞَّ ﻋَﻦْ ﺳَﺒِﻴﻠِﻪِ ۖ ﻭَﻫُﻮَ ﺃَﻋْﻠَﻢُ ﺑِﺎﻟْﻤُﻬْﺘَﺪِﻳﻦ

     

    Kayi Kira Zuwa Ga Hanyar Ubangijin Ka Da Hikima Da Wa’azi Mai Kyau Kuma Kayi Jayayya Dasu Da Magana Wadda Take Mafi Kyau Lalle Ne Ubangijin Ka Shine Mafi Sani Ga Wanda Ya Bace A Hanyar Sa Kuma Shine Mafi Sani Ga Masu Shiryuwa

     

    ALLAH YASAKA DA ALKAIRI PROFESSOR ALLAH YAKARA YAWAN ILMI DA BASIRA DAN ALFARMAR MANZON ALLAH (SAW). AMIIIIN

    Share
  • Watarana ANNABI (S.A.W) Yana Tafiya a Bayan Garin Madina, Sai Ya Ji An Kira Shi: Ya ANNABIN ALLAH (S.A.W)!

    Watarana ANNABI (S.A.W) Yana Tafiya a Bayan Garin Madina, Sai Ya Ji An Kira Shi: Ya ANNABIN ALLAH (S.A.W)! Ya ANNABI ALLAH (S.A.W)!

     

    Sai ANNABI (S.A.W) Ya Duba Baya Bai Ga Kowa Ba Sai Ya sake Jin Kiran Sai Yabi Inda Sautin Yake Fitowa.

     

    Da Ya Isa Wajen Sai Ya Iske Wata Barewa a Daure, a Gefe Kuma Ga Wani Balaraben Kauye Yana Kwance Yana Barci.

     

    Sai Barewa Ta Ce Da Shi: “Ya RASULULLAHI! Wannan Mutumin Ya Farautoni Alhali Ni Ina Da ‘Ya’ya Guda Biyu a Wancan Kogon Dutse, Ka Taimaka Min Ka Sake Ni Na Je Na Shayar Da Su Nono Sannan Na Dawo”

     

    Sai ANNABI (S.A.W) YaCe:”Anya! Kuwa Zaki Dawo?”

     

    Sai Barewa Ta Ce”Idan Har Ban Dawo Ba ALLAH Yayi Min Azabar Da Zai Yiwa Mai Cin Rashawa”

     

    Sai ANNABI (S.A.W) Ya Kwance Ta Tafi.

     

    Da Barewa Ta Cika Alkawari Ta Dawo

    Sai ANNABI (S.A.W) Ya Kama ‘Kafarta Yana Kokarin Daureta Da Igiya Sai Balaraben Kauye Nan Ya Farka Daga Bacci,

     

    “Kai Ne Fansar Uwata Da Ubana Ya Manzon ALLAH.

     

    Ni Ne Na Farauto Ta Ko Kana Da Bukata.?”. Inji Wannan Balaraben Kauyen

     

    Sai ANNABI (S.A.W) YaCe: “Na’am! Ina Da Bukata”

     

    Sai Balaraben Qauyen Nan Yace: “Na Baka Ita Ya RASULULLAHI”

     

    Sai ANNABI (S.A.W) Ya Saketa Ta Koma Wajen Ya’yanta Tana Tafiya Tana Cewa:

     

    “Na Shaida Babu Abin Bautawa Da Gaskiya Sai ALLAH. Na Kuma Shaida ANNABI MUHAMMAD MANZON ALLAH Ne”.

     

    DARASI:-

    Jama’a Idan Muka Duba Da Idon Basira Zamu Ga Abubuwan Da Wannan ‘Kissa Take Koyarwa Sune Kamar Haka:-

     

    1. CIKA ALQAWARI

     

    2. TSANANIN TAUSAYIN UWA AKAN ‘YA’YANTA

     

    3. NEMAN HALAL TA HANYAR FARAUTA

     

    4. DABBOBI KANSU NA TSORON AZABAR MAI CIN RASHAWA.

     

    YA ALLAH! KA QARAMANA SOYAYYAR ANNABI S.A.W BIJAHI S.A.W. AMEEN

     

    Via Umar Chobbe

    Share
  • KISSA: Kissar Wata Mata Tsohuwa A Zamanin Manzon Allah SAW.

    A Zamanin ANNABI (S.A.W) anyi wata mata tsohuwa mai masifar rikici da raki, ita wannan mata ta kasance kullun saita kawo kara gurin ANNABI (S.A.W) cewa anyi mata kaza, ko tace masa yara sun takura mata.

     

    Ana cikin haka wata rana ta shigo gidan ANNABI (S.A.W) domin takai masa kara, tana shiga saita tarar da killishi a gabansa, sai tace menene wannan sai yace mata kilishi ne, bayan ta gaya masa matsalarta, kafin ta tashi sai ya dauko kilishin yace ga wannan naki ne

    .

    Sai wannan tsohuwa tacewa fiyayyen halitta, kaga bakin nawa babu hakora bazan iya taunawa ba,

    .

    Sai ANNABI (S.A.W) ya karbi kilishin ya saka a bakin sa, ya ciccira mata yadda zata iya taunawa,

    .

    Sannan sai ANNABI (S.A.W) ya mika mata Tsohuwa ta dauki kilishin ta fara ci

    .

    A take a wurin sai anji ta fara yin salati ga ANNABI (S.A.W)

    .

    Bayan kwana biyu sai daya daga cikin matan ANNABI (S.A.W) suke tambaye shi cewa:

    .

    Ya ANNABIN ALLAH yanzu wannan tsohuwar sai dai kawai ta shigo gidan tana salati kawai, kuma ta gaishemu ta koma, amma ta daina kawo karar kowa?

    .

    Sai ANNABI (S.A.W) yace kun manta da

    ranar dana bata kilishi?

    .

    Sai matan suka ce kwarai kuwa mun tuna da wannan Ranar!

    .

    Sai ANNABI (S.A.W) yace to ai Albarkar nyawun dake bakina ne wanda ya taba

    kilishin Shine ALLAH ya kawar mata da duk wata damuwan ta anan duniya.

    .

    Kaji fiyayyen halitta kenan. Umar chobbe ne ke gaisheka Ya Rasulullah

    .

    YA ALLAH ka BAMU ALJANNA ALBARKAN NYAWUN BAKIN ANNABI MUHAMMAD (S.A.W).

    .

    Ya Allah kasa Albarkan Nyawun ANNABI S.A.W Ya Kawar Mana da Dukkan Damuwanmu Duniya da lahira Muma Bijahi S.A.W. Amiin

    Share
  • Wata Rana Wani Dattijo Yana Tafiya(Tare Da Muqarrabansa), Suna Cikin Tafiya Sai Suka Biyo Ta Wajen Wani ‘Kududdufi.

    Wata Rana Wani Dattijo Yana Tafiya(Tare Da Muqarrabansa), Suna Cikin Tafiya Sai Suka Biyo Ta Wajen Wani ‘Kududdufi, Dattjon Nan Ya Tura Wani Daga Cikin Muqarraban Nan Nasa Da Yaje Ya ‘Debo Masa Ruwa(a Wancan ‘Kududdufin) Saboda Yana Jin ‘Kishirwa.

     

    Wanda Aka Aika ‘Din Ya Tashi Yaje Don Ya ‘Debo Ruwan Kamar Yadda Dattijon Nan Ya Bukata, Zuwansa Ke Da Wuya Sai Ga Wani ‘Dan Maraqi Ya Shigo Cikin Ruwan Shima Zai Sha, Saboda Haka Sai Ya Zama Duk Ya Dagula Ruwan Laka Da Ta6o Duk Suka Canjawa Ruwan Kala/Launi.

     

    Wannan ‘Dan Aiken Yayi Tunanin Cewa:”Ta Yaya Zan Kaiwa Dattijon Nan Wannan Ruwa Mai Datti???”, Sai Ya Dawo Ba Tare Da Ya ‘Debo Ruwan Ba Yake Shaidawa Dattijon Nan Cewa; Ruwan Ne Wani Maraqi Shiga Ya Damashi Duk Datti Ya Taso Shi Yasa Bai ‘Debo Ba, Bayan Ya Jira Zuwa Wani ‘Dan Lokaci, Sai Dattijon Nan Ya ‘Kara Tura Wannan Mutumin Da Yaje Da Farko Akan Ya Koma Ya ‘Debo Masa Ruwan, Ya Koma Nanma Ya Ga Har Yanzu Dai Ruwan Akwai Dattin. Ya Dawo Ya Sanar Da Dattijon Nan Haka.

     

    A Karo Na Uku Ya ‘Kara Umartar Wannan Mutumin Da Yaje Ya ‘Debo Ruwan, Da Yaje Kuwa Sai Ya Tarar Da Dattin Ya Kwanta ‘Kasa, Ruwan Ya Zama Fari Tas Mai Hasken Gaske. Sai Ya Sanya ‘Kwaryarsa Ya ‘Debo Ruwan Ya Kawowa Dattijon Nan.

     

    Dattijon Nan Ya Kalli Ruwan Sannan Ya ‘Daga Kai Ya Kalli Mutumin Nan Da Ya Aika Ya Ce Masa:”To Kalli Abin Da Ka Yi(Hakuri) Har Ka Sanya Wannan Ruwan Ya Zama Mai Tsafta, Kai Yi Hakuri Har Ka Bari Ya Kwanta Sannan Ka ‘Debo. Don Haka, ZUCIYARKA(Ko Kuma In Ce Ranka/Ruhinka) Ma Haka Take, Lokacin Da Take Zama Cikin ‘Kunci Da Damuwa(Wani Ko Wani Abu Ya Dagula Maka Ita), To Ka Bata ‘Dan Lokaci Qalilan Zata Zama Mai Kyau Da Tsafta Ta Kuma Samu Nutsuwa.

    Ba Lalle Sai Ka Sanya Mata ‘Karfi Ba Ko Takurata Wajen Nutsar Da Ita. A’a Idan Ka Samu Kanka a Cikin Irin Wannan Yanayin Na ‘Bacin Rai Ko Fusata Ko Dai Wani Abu Makamancin Hakan; KA TUNA CEWA DA AMBATON ALLAH TA’ALA DUKKAN ZUKATA KE SAMUN NUTSUWA, SAI KA MAI DA LAMURANKA GA ALLAH TA’ALA TA HANYAR YAWAITA AMBATONSA DA KUMA NEMAN GAFARARSA.

     

    ALLAH Ta’ala Yasa Mu Zamto Cikin Zakirai a Ranar Da Dukiya Bata Amfani Balle ‘Yaya Ameeeeeeen.

     

    Othman Muhammad

    Share
Back to top button