LABARU

  • Almajiranci A Najeriya: Laifin Gwamnati Ko Iyayen Yara Waye Mai Laifi ???

    LAIFIN IYAYE KO GWAMNATI ???

     

    Laifin Duk Na Bangarorin Duka Biyu Ne.

     

    Na Farko …..

     

    Gwamnati ke da alhakin sanin yanayin karfin iyaye, kafin suyita haihuwa iri iri…

     

    Dolene gwamnati tasan Yaya muranen Karkara ke rayuwa, don su fa suna haihuwar Machineries ne na Noma ba wai yaya ba…to amma gwamnati bata aikata hakan.

     

    Mafi yawan Yayan da suke bara a gari daga kauyuka suke zuwa.

     

    Dolene don magance haka gwamnati ta san meke gudana a karkara don fitar da tsarin taimaka musu da kuma kayyade iyalai ko samar da hanyar daukar nauyinsu. Amma kash Gwamnatu ba tasu take ba…

     

    Na Biyu ….

     

    Mafi yawan Iyayensu na cikin duhun Jahilalci, su a wurinsu tarun Yaya abun alfahrine, don yawan Yayanka yawan girman gonarka…

     

    To zasuyita aure don su tara masu musu ayyuka da kuma fita kunya…

     

    A karshe kuma Malamansu ma nada gudumowa akan hakan, don su kan fita kauyuka da kansu don neman a basu Yara wadda a karkashin haka suna bautar dasu…wajen

     

    * Noma

    * Rubutun sha na kudi

    * zuwa wajen Sauka da sauransu…

     

    Amma lallai Tsarin karatun Almajirancin na bukatar gudumowar Gwamnati da kuma iyaye baki daya. Allah ya kawo mana sauki. Amiiiin

     

    Daga: Kabiru Special

    Share
  • Wani Bawan Allah Ya Ginawa Yan Tijjaniyya Katafaren Madaukakin Baki A Gombe.

    Wani Bawan Allah Ya Gina Katafaren Masaukin Baki Wa Yan Darika Fisabilillah A Gombe.

     

    Wannan bawan Allah mai Suna Alhaji Muhammadu Adamu Kashere ya gina kawataccen gida na zamani fisabilillah don sauke baki da suke zuwa daga kasar Morocco da Senegal dama bakin mu na cikin gida najeriya.

     

    Masaukin bakin ya kunshi bangarori daban daban a gidan akwai dakunan kwana da bandaki a kowanne daki, da kuma manyan falo na zamani. Gidan yana kusa da masallacin jumma’a na kungiyar fityanul islam da kuma Makarantar kungiyar dake anguwa uku cikin garin Gombe.

     

    Muna addu’an Allah ya saka masa da alkhairi, ya yawaita mana irin su a cikin al’ummar Musulmai, Allah ya yawaita masa arzikin sa. Amiin.

     

    Daga Babangida A. Maina

    Tijjaniyya Media News

    Share
  • Jadawalin Wuraren Tafsirai Da Sheikh Aminu Under 17 Zai Gabatar Watan Ramadana 2023.

    ASSALAM ALAIKUM WA RAHMATULLAHI WA BARAKATU

     

    As’habu Addaawah Assaqafihya Attijaniyya Wannan qungiya mai suna a sama tana sanar da yan uwa musulmai zuwa wajan budi karatun TAFSEER Wanda shugaban ta Sheikh

    Aminu under 17 garkuwan faila zai fara kamar haka;

     

    Ranan 29/8/1444 22/3/2023

    Guraran da za’a gudanar Kamar haka

     

    (1) Zawiyan Sheikh Aminu under 17 garkuwan faila ring Road layin na manzon Allah SAW Street karfe 5:40am bayan Sallah Asuba zuwa 6:40am

     

    (2) Rafinfa kwanan shagari qarfe 9:40am na safiya zuwa 10:40am

     

    (3) Gidan madora Adebayo karfe 2:30pm bayan Sallah azahar zuwa 4:00pm

     

    (4) kasuwar katako karfe 4:30 pm bayan Sallah la’asar zuwa 5:30pm

     

    (5) Zinariya masallacin Abu huraira karfe 8:35pm zuwa 10:00pm na dare.

     

    Allah yaba da ikon zuwa, Allah yasa a fara Azumi lafiya yasa mu dace, Da Albarkan sa da falalansa, Ya karbi duk ibadun mu daga farko har karshe.

     

    Allah ya kara tsira da aminci da wasila da fadilah ga shugaban mu Annabi Muhammad S A W har da iyalan sa gaba daya.Ameen

     

    Sanarwa Daga;

    Shiekh Aminu under 17 Garkuwan Faila Jos

    Share
  • Muna ALLAH Wadai Da Cin Mutuncin Almajiranci A Tashar Arewa 24.

    MUNA ALLAH WADAI DA MANA KISAR DA AKE MA ALMAJIRAI A WANNAN SHIRI “MANYAN MATA”

     

    Bama musawa, lallai duba ga yanayin chanjawar zamani da bukatar samun gyare-gyare a harkar Almajiranci, amma irin wannan salo da tashar @Arewa 24 ke bi na kokarin cusa kyamar harkar Almajiranci a tunanin al’umma ta hanyar amfani da irin wadannan fina-finai da ake nuna Almajirai ne ke rikidewa su dawo bata gari dake addabar Al’umma, lallai wannan wani yakine shiryayye da aka tunkari Almajirai da shi, kuma babban manufar shine yaki da karatun Alkur’ani.

     

    A mai-makon su shagala da shirya Fim wanda ciki za su ke jan hankalin Shugabanni akan su kula da harkar Almajiranci ta hanyar sanya hannu wajen tallafawa sha’anin, amma sai al’amarin na su ya zamo Almajirancin suke son yaka kai tsaye su kawar da shi.

     

    Muna masu kiransu da yaren da zasu fahince mu, lallai da bukatar su dakatar da wannan mummunan kudurinsu na su na kwangilar Yahudawa, domin lallaine ba’a kawo gyara ta hanyar muzantawa da kuma cin fuskar wadanda ake so a gyarawa.

     

    MUNA FATAN SAKON MU ZAIJE GARESU, KUMA ZASU DAUKI MATAKIN KAWO GYARA.

     

    Daga: Muhammad Usman Gashua.

    Share
  • Za’a gina babban katafaren cibiyar haddar Alkur’ani mai girma ta zamani a jihar Bauchi mai suna “Sheikh Dahiru Usman Bauchi RA”

    ALBISHIRIN KU MUTANE SHEIKH DAHIRU BAUCHI RA.

     

    Za’a gina babban katafaren cibiyar haddar Alkur’ani mai girma ta zamani a jihar Bauchi mai suna “Sheikh Dahiru Usman Bauchi RA” wanda mai girma gwamnan jihar Bauchi Bala Abdulƙadir Ƙauran Bauchi ta dauki nauyin ginawa.

     

    Gwamnan jihar Bauchi Senator Bala Abdulƙadir Ƙauran ya fadi hakan ne, a yayin da yakai ziyara girmamawa ga babban malamin a gidan sa dake titin Bauchi zuwa Gombe, inda ya tabbatar da fara aikin cikin kan-kanin lokaci da rardan Allah.

     

    Muna alfahari da wannan katafaren aiki, Muna addu’an Allah ya saka masa da alkhairi, ya karawa Maulana Sheikh lafiya da nisan kwana albarkacin Manzon rahma SAW. Amiiiin

     

    Babangida Alhaji Maina

    Tijjaniyya Media News

    Share
Back to top button