MAULUD

  • Babu gurin da nake jin dadin kasancewa kamar gurin Maulidin Manzo S.A.W ” ~ Sarkin Bichi

    Babu gurin da nake jin dadin kasancewa kamar gurin Maulidin Manzo S.A.W ” ~ Sarkin Bichi

     

    Mai Marataba Sarkin Bichi, Alh. Nasiru Ado Bayaro, ya ce babu wajen da yake jin dadin kasancewar sa a Duniya face wajen taron Maulidin Annabi S.A.W.

     

    Alh. Nasiru Ado Bayero, ya bayyana hakane a daren Asabar a wajen taron Maulidin da Mahmud Sa’eed Adahama, ya shirya a Unguwar G.R.A da ke Kano.

     

    Mai Martaban ya ce, ” ba karamin farin ciki yake ji ba, idan akace ya halarci taron maulidi “.

     

    Daga cikin wadanda suka halarci Maulidin, akwai Shugaban majalissar Shura ta jihar Kano, Sheikh Malam Ibrahim Khaleel, inda ya ce rashin shugabanci na gari da bin doka da Oda da kyakkyawar mu’amula, wasu muhimman abubuwa ne da sai an gyara su za’a samu Al’umma ta gari.

     

    Taron Maulidin da aka gudanar cikin Sa’o’i dai, ya maida hankali ne kan kara bayyanawa Al’umma daraja da girman da Manzo S.A.W ke da shi a wajen ALLLAH madaukakin Sarki, kamar yadda masu jawabi su kayi.

     

    Daga Nazeer Bashir Tsamiya.

    Share
  • Wata Rana An Tambayi Maulana Sheikh Ibrahim Inyass (Ra) Menene Hujjan Yin MAULUD ?

    Farfesa Ibrahim Maqari Yana Cewa;

     

    Wata rana an tambayi Maulana Sheikh Ibrahim Inyass (Ra) menene hujjan yin MAULUD ?

     

    Sai Shehu yace rashin Hujja Maulidi shine ya kawo hujjan mu na yin mauludin Domin akwai Abunda yafi Qarfin hujja Shehu yace baka ga duk Qur’ani, ba inda Allah yacema UWA ta so DAN ta ba ?

     

    Ai Allah bai cema UWA ta so DAN taba, saboda bata bukata sai ance mata ta so shi zata so shi. Domin Allah ya riga ya shuka son DAN acikin UWAN, Amma shi DAN da a kasan zai iya Qin biyayya baka ga wuri daban daban Allah yake umartarsa da bin iyaye ba?

     

    SHARHI

     

    PROFESSOR IBRAHIM MAQARI yana cewa: Watarana an taba haduwa da wata mata aka nunamata wani malami “imamul Faharrazi” aka ce mata kinga malamin can zai iya baki Hujja dubu akan samuwan Allah

     

    Sai matan tace “Allah sarki miskini!

     

    Ai yana da shakka dubu ne a zuciyarshi shiyasa har zai iya samo hujja dubu in ba haka ba ya za’ayi mutum, in ba mahaukaci ba yadauko “touch light” da rana kuma yace wai yana neman Rana.

     

    Duk girman hujja ai bata kai “touch light” rana tare da ubangiji ba, Allah da yakira kansa “Azzahiru” kuma yake bukatan wata hujja tazo ta bayyana dashi ? Ai Lamarin Akwai Abun dubawa

     

    Allah yakarawa PROFESSOR lafiya da fahimta bijahi S.A.W. Amiin Yaa Allah

    Share
  • MANZON ALLAH (S.A.W) Ba Irinmu Bane, Domin Da Kansa Yake Cewa.. ‘Ayyukum Ka Hai’atiy. Inji Sheikh Farfesa Ibrahim Maqari

    SHEIKH (Prof.) IBRAHIM AHMAD MAQARY (R) Yana Cewa:

     

    “MANZON ALLAH (S.A.W) Ba Irinmu Bane, Domin Da Kansa Yake Cewa… ‘Ayyukum Ka Hai’atiy???

     

    Ma’ana: Wanene Ke Da Structure Irin Tawa???”.

     

    To Kuma Gaba ‘Daya Wadanda Suka Kafirce Ma Annabawansu Sun Kafirce Ne Saboda Sun ‘Dauka Kuma Sun Ce Annabinsu Mutum Ne Kamarsu…”,

     

    ‘Yan’uwa Mu Kula… A Kula… ANNABI Ba Irinmu Bane.. Halitta Ne Wanda a Hadisin Bukhari Aka Ruwaito Cewa:

     

    Lokacin Da SAYYIDUNA ALI(R.A) Ya Hau Kan Kafadarsa Lokacin FATHU MAKKAH Sai Da Ya Ga Kamar Zai Iya ‘Dauko Taurarin Sama,

     

    Ku Duba Tsawon Ka’aba Amma SAYYIDUNA ALI (R.A) Yana Hawa Kafadan ANNABI (S.A.W) Ya Ciro Wadannan Gumakan Kuma Ka’aba Kowa Ya San Tsawonta Dai… A Nutsu/Kula Dai”.

     

    LA ILAHA ILLALLAH…

     

    ALLAH YA ‘KARA TSARE MANA IMANINMU, YA ‘KARA MANA ‘KAUNAR SAYYIDUL-WUJUDI (S.A.W) AMEEEN

    Share
  • IBLISA” SHINE SHUGABAN MAZHABAR MAKIYA MAULUDIN MANZON ALLAH (S.A.W)..?

    KO KASAN DA CEWA “IBLISA” SHINE SHUGABAN MAZHABAR MAKIYA MAULUDIN MANZON ALLAH (S.A.W)..?

     

    Imam Ibn Kathir ya kawo Hadisi a littafinsa Albidaya Wannihaya, Mujalladi na 2 Shafi na 166, kamar haka:-

     

    أن إبليس رن أربع رنات حين لعن وحين أهبط وحين ولد رسول الله صلى الله عليه وسلم وحين أنزلت الفاتحة

     

    Ma’ana: Lallai ne Iblisa yayi kururuwar kokayya sau hudu, Lokacin da aka la’anceshi, da lokacin da aka fitar da shi (Daga Aljannah) da lokacin da aka Haifi MANZON ALLAH (S.A.W) da kuma lolacin da aka sauke Fatiha.

     

    A rike lissafin

     

    Duk yadda aka kai ga chanja zance da boyewa gaskiyar da take bayyana shi ne, nuna bakin ciki akan nuna farin ciki da haifuwar MANZON ALLAH (S.A.W) bakin ciki ne ga samuwarsa (S.A.W), tunda a yau ta kai har bomb ake tadawa cikin taron Masu Mauludi a wata kasa, a yayin da yan uwansu na nan suke farin ciki da hakan.

     

    IDAN HAR YANA DAGA CIKIN ABABEN DA SUKA SANYA IBLISA KUKA DA KURURUWA, BAKIN CIKI DA HAIFUWAR MANZON ALLAH (S.A.W), TO ANYA KUWA MASU KURURUWA YAU AKAN KIYAYYAR FARIN CIKI DA HAIFUWARSA (S.A.W) BA SUNE HAKIKANIN YAN MAZHABIN SHAIDAN BA…?

     

    Kar kayi mamaki dan uwa, domin ANNABI (S.A.W) ya fadi a hadisi sahihi cewa “Kahon Shaidan zai bayyana a Najadu” Malamai sunyi ittifaki akan wannan kahon Shaidan din shine “IBNU ABDULWAHAB ANNAJADI”.

     

    Shine Malami guda a tarihin Musulunci da yake yaki da yin Mauludi, kuma Almajiransa (WAHABIYAWA) suka sunnatu akan hakan, domin shine wanda ya aiwatar da ta’addanci akan Sharifai a Makkah da Madina ya karkashesu, ya karbe jagoranci daga garesu ya dankawa Ahli Sa’ud, kuma ya hani da ko a bayan kiran Sallah kada ayi salati ga MANZON ALLAH (S.A.W), kuma shine yake taya Shaidan aiki wajen son ganin an kira Musulmi da sunan Kafirai, Mushrikai, Yan Bidi’a, domin adadin yan wuta ya linka yan Aljannah a Al’ummar MANZON ALLAH (S.A.W) kamar dai yadda Almajiransa ke yin da’awa a salon hakan a yau.

     

    SABODA HAKA A TAKAICE DUK WANDA KAGA YANA KIN MAULUDI A YAU DAYAN BIYU NE, KO WANDA AKA RIBATA CIKIN JAHILCI, KO KUMA WANDA YAKE TAYA MAI GIDANSHI IBLISA BAKIN CIKI DA SAMUWAR MANZON ALLAH (S.A.W).

     

    ALLAH KA TSARE MU DA BIN TAFARKIN SHAIDAN DA AYARINSA.

     

    Daga: Muhamad Usman Gashua

    Share
  • MASHA’ALLAH; Annabi Muhammad (SAW) Shi Ya Fara Yin Maulidi – Cewar Sheikh Ahmadu Zaria.

    Annabi Muhammad (SAW) Shi Ya Fara Yin Maulidi – Cewar Sheikh Ahmadu Zariya.

     

    Daga Idiris M Usman (Daddy Big’ja) Zariya

     

    Shahararren Malamin Addinin Musulunci Mai Suna Ahmadu Madahun Nabiyi Zariya ya bayyana cewa ƙago wani Sabon Abu a cikin Musulunci bai taɓa zama haramun ba face halastaccen Abune.”

     

    Shehin Malamin ya ƙara da cewa Annabi Shine ya fara yin Maulidi domin yazo a Hadisai kuma Allah bai hana Maulidi ba duba da bai zo a Al-Qur’ani cewa abune Haramun.

     

    Bugu da ƙari Sheikh Madahu ya ci gaba da cewa Allah (SWA) ya kawo ƙissan Maulidin Annabi Isah (AS) dakansa Acikin Al-Qur’ani bare kuma dan Musulmi suna kwaikwayo da Hakan sai ya zama haramtaccen Abu ? Don sun yi Maulidin Annabi Muhammadu (SAW).

     

    Allah ya barmu da soyayyan Annabi ﷺ. Amiin

    Share
Back to top button