NASIHA

  • Wani Abin Al’ajabi Daya Faru Da Sheikh Ibrahim Inyass RA A Duniya.

    Wani Abin Al’ajabi Ya Taɓa Garuwa Da Wani Baƙar Fata Musulmi Daya Jijjiga Duniyar Ilimin Manyan Malaman Larabawa Da Turawa Na Addinin Musulunci.

     

    Wannan ita ne babbar jami’ar musulunci ta duniya Al Azhar ta Egypt, dake ƙasar Masar jami’ar tafi shekara dubu ita ne kuma ta farko a duniyar musulunci, sannan har yanzu ita kejan kambun babbar jami’ar musulunci ta duniya,.

     

    Jami’ar musulunci sai ta aikowa ta kira wani babban malamin addinin Musulunci baƙar fata ɗan Africa bayan ta gama yi masa jarabawa da tantancewa duk yadda zasu iya da duk wata ƙwarewa ta ilimi mai zurfi mai makon ta bashi ijaza sai ta bashi mukamin Shaykhul Islam na duniya gaba daya.

     

    Sannan suka sashi gaba ya jasu sallar jumu’a baƙar fata daga wata ƙasa irinsa na farko a Duniya. Wato dai ya zamo uba ko nace baban masu lashe interview da jarabawa na Duniya,. Sannan abune daya faru shiyasa baza mu faɗi sunan da kanmu ba, Koza ku faɗa mana sunan sa a kwament?.

     

    Yanzu haka dai ko yanzu a Nigeria ɗaliban sa biyu ɗaya babban malamin hadisi ne na Duniya ɗayan kuma fitaccen mai tafsirin Alqur’ani mai girma ne.

    Share
  • Banbancin Masu Shirya Tarukan Walimar Siyasa Da Tarukan Mauludi

    KU SUFAYE KU GODEWA ALLAH.

     

    Idan ka dauki dubban kudade ka baiwa biri, da kwayar Ayaba guda, mai yiwuwa sai ya yayyage wadannan kudaden, ya dauki Ayaba guda, alhali wadannan kudaden zasu sayi dubban Ayaba da zai dauki lokaci yana mora.

     

    To amma kai da kasan amfanin Kudaden, kaga idanunka basu ma zuwa kan wannan Ayabar guda, balle ka shagala da ita.

     

    To haka abin yake ga wadanda suka fahimci girman MANZON ALLAH (S.A.W) suke Shirya tarukan Mauludinsa, da wadanda suka fahimci girman wasu ababen Duniya suke shirya tarukan nuna murna akansu, ta hanyar kyarar yi ga MANZON ALLAH (S.A.W).

     

    Yadda bazaka iya ganar da Birrai gane Muhimmancin kudaden nan sama da Ayaba guda ba, haka zalika suma wadannan bazaka iya ganar dasu Muhimmancin nuna soyayyar MANZON ALLAH (S.A.W) da godewa ALLAH a wannan Janabi sama da wanin hakan ba.

     

    Face dai yadda wadannan Birran zasu yayyaga wadannan kudaden, suma haka zasuke yayyaga muku mutunci saboda nuna soyayyarku ga madaukakin da babu kamarsa.

     

    KU GODE ALLAH DA ALLAH YA ZABE KU YA FAHINTAR DA KU GANE GIRMAN WANDA YAKE GIRMAMAWA, KUMA KU ROKAR MUSU ALLAH SUMA YA GANAR DA SU GANE HAKAN. AMIIIIN YAA ALLAH.

     

    Daga: Muhammad Usman Gashua

    Share
  • ZABEN 2023: Kowa Yake Ya Zabi Wanda Yake So, Amman Ku Zabi Shugaba Nagari. Inji Sheikh Dahiru Bauchi OFR RA.

    YA DACE JAGORORIN KUNGIYA SU NAKALCI IRIN WANNAN HIKIMAR WAJEN JAGORORIN SUFAYE.

     

    A zabukan 2011 da kuma 2015 wasu daga Maluman Kungiya sun ayyanawa mabiya yan takarar jam’iyyun da suke so su zaba, karshe dai duk dadin bakin da sukayiwa mabiya aka fuskanci akasinsa kowa yaji a jikinsa, to sai gashi yanzu ma wasunsu na son mai-maita kuskure ta hanyar yin abinda suka yi a baya.

     

    Ka duba jawabi mai cike da wayewa, yadda Maulana Sheikh Shariff Ibrahim Saleh, da Maulana Sheikh Dahiru Usman Bauchi (R.T.A) suka fayyacewa dukkanin mabiya akan, kowa ya zabi wanda ya kwanta masa a rai, wanda hakan matakine da babu wani guda da zai kuka dasu har abada, idan aka samu akasi a mulkin wani shugaba da ace sun ayyana shi.

     

    ALLAH YA GANAR DA JAGORORIN WAHABIYA GA RUNGUMAR WANNAN HIKIMAR, WALA’ALLAH SA RAGE DUMLMIYAR DA MABIYA. AMIIN YAA ALLAH.

     

    Daga: Muhammadu Usman Gashua

    Share
  • Ni Bani Da Wani Ɗan Takara Ɗaya Tak Da Zan Zaba. Inji Sheikh Dahiru Usman Bauchi OFR

    PRESS RELEASE;

     

    Zantawar MAULANMU SHEHU TAHIRU (R.A) Da ‘Yan Jaridu a Jiya Litinin 20-02-2023

     

    “INA SON KOWA YA FITA YA ZAƁI WANDA YAKE SO, DON NI BA NI DA WANI ƊAN TAKARA” – SHEIKH DAHIRU USMAN BAUCHI.

     

    Babban Shehun Ɗarikar Tijjaniyya a Najeriya Shehu Ɗahiru Usman Bauchi Ya Ce; Ba Shi Da Wani Ɗan Takara Ɗaya Tak Da Zai Ce a Zaɓa a Babban Zaɓen Shugaban Ƙasa a Najeriya Da Za a Gudanar a Ranar Asabar Mai Zuwa.

     

    Shehu Ɗahiru Usman Bauchi Wanda Ya Ke Amsa Tambayoyi Daga Manema Labaru a Abuja Ya Ce; Shi Kowa Na Sa Ne a ‘Yan Takarar, Don Haka Ya Ke Bukatar Jama’a Su Yi Amfani Da Hankalinsu Wajen Zabar Wanda Su Ka Ga Ya Dace a Babban Zaɓen.

     

    Kazalika Malamin Ya Yi Fatan Duk Wanda Ya Lashe Zaɓen Ya Zama Sabon Shugaban Najeriya To Ya Mai Da Hankali Wajen Kawo Hanyoyin Da Talakawa Za Su Samu Sauƙi Daga Ƙuncin Tattalin Arzikin Da Ake Fama.

     

    “Gwamnatin Nan Da Mu Ka Fito, Ba Mu Ji Daɗin Ta Ba, Akwai Abubuwa Da Yawa Na Matsuwar Mutane a Zamaninta, Wanda Ba Mu Ji Daɗinsu Ba, Kamar Tsare(Rufe) Ƙasa a Hana Komai Shiga, Na Ciki Kuma Ba Ya Isa, Mu Ne Talakawa ‘Yan Ƙasa Ba Mu Ji Daɗin Waɗannan Ba.”

     

    Malamin Ya Gabatar Da Addu’ar Zaman Lafiya Mai Ɗorewa a Najeriya Ya Na Mai Yabawa Manema Labaru Da Yanda Su Ke Aikin Isar Da Saƙonnin Wayar Da Kan Jama’a.

     

    (©️Mai Rahoto/Rubutawa; Nasiru Adamu El-Hikaya, VOA Hausa).

     

    Ameeeen, Ameeen SHEHU(R.A).

     

    ALLAH Ya Kara Maka Lafiya Da Nisan Kwana, Ya Sa Mu Kammala Waɗannan Zaɓuka Da Muka Saka a Gaba Lafiya, Ya Bamu Mafi Alkhairi, Don Albarkar SHUGABA(S.A.W) Amiiiin

     

    Daga: Othman Muhammad

    Share
  • Nasiha Mai Matukar Muhimmanci Ga Daukacin Al’ummar Musulmai Baki Daya.

    YI KOKARI KA KIYAYE WANNAN.

     

    Daga MALAM UMAR SANI FAGGE

     

    (1). Karka rinka yin fitsari a wurin da kake yin wanka, domin hakan yana gadar da yawan

    mantuwa.

     

    (2). Karka rika kwantawa barci bayan ka

    cika cikinka da abinci, domin yin hakan yana

    gadar da mutuwar zuciya.

     

    (3). karka rika yawaita kallan al’auranka ko ta wasu, domin yin hakan yana sa dakikanci

    da nauyin kwakwalwa wajen fahimtar abubuwa.

     

    (4.). kar karika yin bacci bayan sallar

    asuba har sai rana tafito, domin yin hakan na

    janyo tsiya da talauci.

     

    (5). kar ka sha madara bayan kaci kifi, domin yin hakan yana gadar da kuturta.

     

    (6). karka ci ko sha alhali kana da janaba, domin yin hakan makarohi ne, kuma yana jawo

    raunin jiki.

     

    (7) karka rika hassada ko munafunci da

    ha’inci, domin suna da hatsari ga lafiya, sukan

    kuma haifar da cutar hauka, gashi kuma suna

    bata ayyuka masu kyau.

     

    (8).karka rika yawan kukan babu ko ka yi ta tallan talaucinka afili. Yin hakan yakan dawwamar da mutum cikinsa.

     

    (9) karka rika kwanciya barci alhali kana jin fitsari, yin hakan yana haifar da mutuwar

    mazakuta.

     

    10. Duk wanda yadau hannunsa mai albarka ya tura wannan saqon, ya Allah ka nuna masa manzo( SAW) acikin mafarkinsa. Ameen

     

    Daga: Nauwas Shareef

    Share
Back to top button