NASIHA

  • HUDBAR ANNABI MUHAMMADU (S.A.W) A KAN WATAN AZUMIN RAMADAN

    HUDBAR ANNABI S.A.W A KAN WATAN AZUMI

    DAGA TASKAR UMAR CHOBBE

     

    Ya Ku Mutane! Hakika watan Allah (Watan Ramalana) yazo muku da albarka da rahama da kuma gafararsa. Wata ne wanda a gurin Allah shine watan da yafi kowane wata, kuma ranakunsa su ne mafiya kyawun ranaku, haka nan dararensa su ne mafiya kyawun darare, kana kuma ranakunsa su ne mafiya kyawun ranaku, sannan kuma awoyinsa su ne mafiya kyawun awowi.

     

    Shi wata ne da ake kiranku zuwa ga bakuntan Ubangiji. A wannan wata an zabe ku ku zamanto masu samun falalar Ubangiji. Numfashinku a cikinsa ibada tasbihi ne. Kuma barcinku a cikinsa ibada ce. Kuma ayyukanku a cikinsa karbabbu ne. Haka nan kuma addu’oinku a cikinsa abin karba ne. Don haka ku roki Allah Ubangijinku na kyakykyawan niyya da kuma tsarkakakkiyar zuciya da Ya ba ku daman azumtarsa da kuma karanta littafinSa. Hakika shakiyyi shi ne wanda aka haramta masa gafarar Ubangiji a cikin wannan wata.

     

    Lalle yayin azuminku ku tuna da yunwa da kishirwar Ranar Tashin Kiyama ta hanyar yunwa da kishiruwan da kuke ji a cikin wannan wata. Ku taimaki fakirai da masakan cikinku. Ku girmama manyanku, kuma ku ji tausayin na kasa da ku, ku sada zumunci a tsakaninku, ku kiyaye harsunanku da kuma ganinku daga abubuwan da basa halalta ku gansu da jinku. Ku ji tausayin marayu don kuma a ji tausayin ‘ya’yayenku a lokacin da suka zama marayu. Ku tuba wa Allah daga zunubanku, ku daga hannayenku sama don rokon Ubangiji a lokutan sallolinku, don wannan (lokacin) shi ne mafi cancantan lokacin da Allah Madaukakin Sarki Ya ke duban bayinSa da rahama, Ya amsa musu idan sun kira Shi, kuma Ya biya musu bukatansu idan sun nema.

     

    Ya Ku Mutane! Kun daure hankulanku da soyace-soyacen zukatanku, don haka ku ‘yantar da su ta hanyar neman gafara. Kun daura wa bayanku abubuwa masu nauyi, don haka ku sauke wannan nauyi ta hanyar tsawaita sujadanku, ku fa san cewa Allah Madaukakin Sarki Ya rantse da daukakansa cewa ba zai azabtar da masu sallah da sujada ba, kuma barai sanya su cikin wuta ba a ranar tashin kiyama.

     

    Ya Ku Mutane! Duk wanda ya shayar da wani mumini mai azumi a cikin wannan wata, to Allah Zai ba shi lada tamkar wanda ya ‘yanta wuyaye da kuma gafarta masa zunubansa da suka gabata. Sai Sahabbai suka ce: Ya ANNABI (S.A.W.) ba dukkanmu ne za mu iya hakan ba! Sai ya ce: Ku kiyaye kawukanku daga koda kuwa ta kwayan dabino ne, Ku kiyaye kawukanku daga wuta koda kuwa da bakin ruwa ne, don kuwa Allah Zai saka kan hakan ga wanda ba shi da wani abin da yafi hakan.

     

    Ya Ku Mutane! Daga cikinku duk wanda ya kyautata dabi’unsa a cikin wannan wata, to yana da lamuni tsallake siradi a ranar da duga-dugai suke zamewa. Haka kuma duk wanda ya saukaka wa abin da hannunsa na dama ya mallaka (bayi) cikin wannan wata, to Allah zai saukaka masa hisabinsa. Duk wanda ya kare sharrinsa cikin wannan wata, to Allah Zai kiyaye shi daga fushinSa a ranar da za su sadu. Kuma duk wanda ya sada zumunci a cikin wannan wata, to Allah Zai isar masa da rahamarSa a ranar da zai sadu da Shi. Haka nan kuma duk wanda ya yanke zumunta a cikin wannan wata, to Allah Zai yanke masa rahamarSa a ranar da za su sadu. Kuma duk wanda ya yi nafilolin salla a cikin wannan wata, to Allah Zai rubuta masa barranta daga wuta. Haka kuma duk wanda ya yi wani aiki na wajibi (farilla) a cikin wannan wata, to Allah Zai ba shi ladan irinsa duba saba’in (70,000) da ya yi a wani watan na daban (wanda ba Ramalana ba). Kuma duk wanda ya yawaita yi min salati, to Allah Zai nauyaya mizaninsa (sikeli) a ranar da mizanai suke fadowa kasa (wato suke dawowa kasa saboda rashin nauyi). Duk kuwa wanda ya karanta wata aya ta Alkur’ani, to yana da ladan wanda ya karanta dukkan Alkur’ani a wani wata na daban.

     

    Ya Ku Mutane! Hakika kofofin aljanna a bude suke a wannan wata, don haka ku roki Allah da Kada ya rufe su a kanku. Haka nan kuma kofofin wuta a rufe suke, don haka ku roki Allah da kada ya bude su a kanku. Kuma shaidanu a kame suke, don haka ku roki Allah da kada su sami galaba a kanku, Allah yasa Damu za’ayi Wannan Azumin Mai Albarka.

     

    Allah ya karbi Ibadun mu gaba daya wanda zamuyi acikin watan mai Albarka

     

    Allah ya gafartamana zunuban mu Gaba Daya Albarkan Annabi S.A.W. Amiin Yaa ALLAH

     

    Daga: Sayyadi Umar Chobbe

    Share
  • Falalar Watan Sha’aban (Nafiloli Da Kuma Zikirai).

    FALALAN AZUMIN WATAN SHA’ABAN DAGA TASKAR UMAR CHOBBE

     

    ANNABI Muhammadu ﷺ yace wanda yayi azumin Alhamis na farkon watan da Alhamis na karken watan sha aban ’’ Wannan Allah zai shigar dakai Aljanna

     

    Annabi yace duk wanda yayi azumi guda daya acikin watan sha aban

    Allah ya haramta jikinka daga shiga wuta kuma zaka zama makocin annabi yusifa acikin Aljanna Kuma Allah zai baka ladan Annabi ayuba da annabi dawudu

     

    Annabi yace idan kuma kayi azumin watan gaba daya Allah zai sauwakye maka mayan mutuwa Kuma Allah zai tun kude maka duhun kabari kuma zai sauwake maka tan bayan Munkarun da nakiri

     

    Kuma Allah zai sanya maka sutura aranan kiyama randa kowa zai tashi tsirara saidai wasu daga cikin bayinshi wanda yatsabesu

     

    Allah mun gode maka daka zuba mana soyayyar Annabi Muhammadu s,a,w Allah kabiya buka tunmu.

     

    Allah duk wanda yaga rubutunnan yayima annabi salati Allah kasa baya mutuwa sai yaje madina ya ziyarci Annabi Dan girma da martaba da kallan da Allah yayima Annabi afadanshi ran israi da mi iraji

     

    Allah ya karbi ibadun mu albarkan ANNABI S.A.W. Amiiiin Yaa ALLAH

    Share
  • JARABAWA CE A HALICCEKA A NAJERIYA ALLAH KABAMU IKON CIN WANNAN JARABAWA.

    BABBAR JARABAWA CE A HALICCEKA A NIGERIA (AREWA) ALLAH KABAMU IKON CIN WANNAN JARABAWA.

     

    Daga Barr Aminu Balarabe Isa.

     

    Babu shakka a halicce ka a Nigeria babbar jarabawa ce.

     

    1- A Nigeria ne (Arewa) zakayi alkhairi 99 amma ayi shiru ayi tsit babu mai yi maka adduar alkhairi da karfafarka akai amma daga ranar da kayi kuskure daya tak za kaga anyi caa akan ka kamar a cinye ka.

     

    2- A Nigeria ne (Arewa) za kaga mutum zai sake maka fuska da dariya amma a zuciyar sa haushin ka yake ji kamar ya kashe ka.

     

    3- A Nigeria ne(Arewa) za kaga mutum yana bada labari a kanka yana hakikan cewa akan wani abu akan ka alhali bai taba ganin ka ba ko kuma bai taba wata hulda da kai ba kawai labari shima yaji akan ka.

     

    4- A Nigeria ne (Arewa) duk mai kudi barawo ne azzalumi ne, amma duk talaka marar ko sisi bawan Allah ne salihi mutumin kirki.

     

    5- A Nigeria ne(Arewa) kowa malami ne mai bada fatawa ne.

     

    6- A Nigeria ne(Arewa) Duk malami talaka shine malamin Allah, amma malami mai rufin asiri ba malamin Allah bane malamin Gomnati ne mai ci da Addini ne.

     

    7- A Nigeria ne (Arewa) ba zaka taba jin an fadi alkhairin Shugaba ba sai bayan ya mutu.

     

    8- A Nigeria ne (Arewa) Zaka ga Limami na jin haushin mamu, mamu na jin haushin Liman.

     

    9- A Nigeria ne (Arewa) za kaga talaka yana tsine wa Shugaban sa wai saboda zalunci amma da Shugaban ya bashi kudi ya rabawa yan uwan sa talakawa sai ya cinye ya danne ya hana su.

     

    10- A Nigeria ne (Arewa) masoyinka shine adali amma abokin adawar ka kuwa duk kirkin sa mugu ne azzalumi ne.

     

    11- A Nigeria ne (Arewa) Zaka ga mutum yana da tarin bukatu sai ya kwana yana barci ya kasa tashi ya fadawa Allah cikin dare amma da safe sai ya je ya fadawa mutum dan uwan sa damuwar sa.

     

    12- A Nigeria ne (Arewa) zaka taimaki mutum daga Allah ya daga shi to yanzu bashi da babban abokin ga ba sai kai.

     

    13- A Nigeria ne (Arewa) kyakkyawan zato yayi karanci amma mummuna kam hmmm sai abin da ya karu.

     

    14- A Nigeria ne (Arewa) yau mutum har ya rasa Wanda zai dauka a matsayin Amini ko masoyi babban aboki saboda ba ka da tabbas akan sirrinka.

     

    15- A Nigeria ne (Arewa) mutum zai ga kayi kuskure ya kasa maka fada ko nasiha amma sai ya fara ya madidi da kai wai kuma abokin ka ne.

     

    16- A Nigeria ne (Arewa) duk lokacin da ka yabi wani Shugaba ko wani mai mulki shi kenan zaka ji ana cewa maula yake aa Neman na miya yake.

     

    Subhanallah.

     

    Inna Lillahi Wa inna ilaihi rajiuun.

    Laa Haula wala Quwwata Illa billah.

    Allah Ubangiji ka bamu ikon cin wannan jarabawa da kayi mana. Albarkan annabi SAW.

    Share
  • MAS’ALAR WAHABIYA SUKA GAZA GANEWA GAME DA MAS’ALAR “TAUSAYI” A LAMARIN ALLAH.

    AN FAYYACE MAS’ALAR DA MALAMAN WAHABIYA SUKA GAZA GANEWA GAME DA MAS’ALAR “TAUSAYI” A LAMARIN ALLAH.

     

    Daga: Muhammad Usman Gashua

     

    Tun bayan fitowar wannan zance mimbaran wa’azin wasu daga Malamai su kai bakuncin Maudu’in tattaunawa na raddi da sauran dangoginsa.

     

    Amma ga wadanda suka kasance masu idanu da kwalli, sun san me Sheikh Nazifi Alkarmawy ike nufi, domin wannan siffa ta rashin tausayi “Insaniyya” kamalace ga ALLAH domin tausayi a fuskar hukunci na daga rauni daga dabi’a ta halitta, face siffa ta ALLAH gusar da abinda tausayi bai iya gusarwa wato jinkai da kuma rahama dake shiryarwa zuwa ga sakamako mai kyau ga bayi ko , Horo da Azaba a fannin Adalcinsa Adalcinsa dake shiryarwa zuwa ga hukunci na jalala.

     

    ALLAH NA DA SIFFOFI NA:

     

    1- Siffa ta Jamala da ke isarwa zuwa ga gafara, jin kai, amfanarwa da kuma jibancin bayi a wannan fuska ALLAH na da sunaye kamar:- Arrahmanu, Arrahimu, Algaffaru, Arraziqu da sauransu.

     

    2- Siffa ta Jalala da ke isarwa zuwa ga hukunci, da kuma martani ga bayi ko wata jarabawa mai taba zuciya kamar sunan sa Al-Muntaqim, Al-mumitu, Ad-Dhar da sauransu.

     

    • Tausayin irin na bayi cike ike da rauni wanda zai haifar da matsala ga abin tausayawa ta fuskar hukunci, hakan kuma abin korewa ne ga ALLAH.

     

    • ALLAH kuma tsarkakke ne ga duk wani rauni da zai haifar da gajiyawa wajen gusar da abinda yake na matsala ga bawa, cikin gafara da jinkansa, ko cikin hukunci da horo ko kuma domin jarabawa ga bayi.

     

    BARA MU WARWARE ABIN A SAUKAKE.

     

    1- Mutum ne Dansa ya samu karaya a kafa, sai ya zamto da an taba wajen sai yaro ya kurma ihu, shin kana ganin iyayen wannan yaro zasu iya daure wannan karaya da wannan yaro ya samu a kafafunsa?

     

    Kaga ba zasu iya ba, wajibinsu su dauke shi su kai shi wajen likita mai dori, a yayin da shi kuma zai ta matsa wannan ciwo wannan yaro na kuka da kururuwa, iyayensa ma na zubda kwalla.

     

    Abin lura anan, shin idan saboda tausayin da iyayen wannan yaro suke ma dansu dalilin halin da ya tsinci kansa ciki, yasa suka ki kai shi wajen gyara shin baka ganin wannan tausayin na su zai zama silar cutarwar ga shi yaron, domin kafar yaron zata lalace karshe ta shafi lafiyarsa baki daya, har ma zai iya rasa rayuwarsa, to yaya abin zai kasance idan madorin yaron shi ma ya kasance yana tausayin yaron irin siffar tausayin iyayensa kaga kenan dai tausayinsa da tausayin iyayen zasu taru su cutar da yaron, amma sai shi madori ya zamo mai kokarin son gusar da ciwo da damuwar da yaron ya samu ta hanyar gyara da koruwar tausayi irin na iyayen yaron ga Dan Nasu.

     

    To haka zalika shi ALLAH ya kan gusarwa bawa abu da zai haifar masa da matsala, ko da ta hanyar gusarwar zukatan wasu zasu sosu.

     

    2- A irin namu dabi’ar, duk uba shi ke da mas’uliyar ciyar da ‘ya’yansa, sai kaga mutum ya tara yara kanana sama da 20 kullum sai ya fita zai samo abinda za su ci, shi ne cinsu, kuma shi ne shansu, lokaci guda sai kaga ALLAH ya karbe shi, sai kaga mutane dangi da yan uwa na kuka saboda tausayin halin da yaran zasu shiga, a yayin da shi kuma mai yiwuwa yana halin farin ciki saboda abinda ya riska na rahamar ALLAH, a gefe guda kuma ALLAH ya tsara wata hanyar da zai ciyar da yaran da su mutane basu san da ita ba, to kaga anan dole a korewa ALLAH siffar tausayi irin wannan na bayi, a kusanto da siffarsa ta Al-warisu, Al-Wali da sauransu.

     

    TAUSAYI A CIKIN BAYI SIFFACE TA KAMALA TA FUSKAR TAIAMAKO TSAKANINSU, TA KAN ZAMA TAWAYA IDAN BA’A AJE TA AN AIKATA ABINDA YA DACE BA KAMAR DAI HIKAYAR MARAS LAFIYA, LIKITA DA MASU JINYA, HAKA ZALIKA JINKAI, GAFARA DA RAHAMA SIFFOFIN DAUKAKA NE GA ALLAH, DA HANYAR AIWATAR DA SU TSAKANIN BAYINSA SIFFAR TAUSAYI IRIN NA BAYI KE KORUWA GARESHI, A GEFE GUDA KUMA ALLAH NA DA SIFFOFI NA JALALA DA YAKE HORO KO AZABA DA SU GA BAYIN DA SUKA RAYU CIKIN ZALINCI

     

    WALILLAHI MASALUL A’ALA, WALLAHU A’ALAM.

     

    ALLAH YA HASKAKA MANA ZUKATA DA FAHIMTAR ADDININSA YA TSARE TSUKE FAHIMTA. Amiin Yaa ALLAH

    Share
  • KISAN MUSULMI A KADUNA: TA’AZIYYA DA JAN HANKALI GA MAHUKUNTA.

    KISAN MUSULMI A KADUNA: TA’AZIYYA DA JAN HANKALI GA MAHUKUNTA.

     

     

    Muna Kira Ga Gwamnantin Tarayya da tayi bincike na gaskiya Akan hakikanin abun da ya faru, kuma ta hukunta masu hannu a cikin wannan lamari.

     

    Lamarin da ya faru a kauyen Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi, Jahar Kaduna.

     

    Muna Addu’ar Allah yajikan su ya gafarta musu ya bawa iyalan su hakuri da juriya na wannan al’amari daya faru, Amin.

    Share
Back to top button