RASUWA

  • Allah Ya Yiwa Daya Daga Cikin Matasan Tijjaniyya Sayyadi Malam Hadi Sheikh Aminu Bakin Kura Bauchi Rasuwa.

    INNA’LILLAHI WA’INNA ILAIHI RAJI’UN

     

    Allah Ya Yiwa Daya Daga Cikin Matasan Tijjaniyya Sayyadi Malam Hadi Sheikh Aminu Bakin Kura Bauchi Rasuwa.

     

    Za’a Gudanar Da Sallar Jana’iza Karfe 4:00pm A Zawiyyar Kidan Sheikh Aminu Bakin Kura, Dake Jihar Bauchí.

     

    Allah Madaukakin Sarki Ya Jaddada Rahma A Gare Shi Ya Gafarta Masa Albarkan SAYYIDINA RASULALLAH S.A.W. Amiiin

     

    Daga: Tijjaniyya Media News

    Share
  • Innalillahi Wa’inna Ilaihir Raji’un, Allah Ya Yiwa Dan Maulanmu Sheikh Ibrahim Inyass Sheikh Muhammad Aqibu Rasuwa.

    Innalillahi Wa’inna Ilaihir Raji’un;

     

    Munyi babban rashi a Khaulaha dake Senegal.

     

    Allah ya yiwa ɗaya daga cikin Ƴaƴan Maulanmu Sheikh Ibrahim Inyass RA rasuwa Sayyadi Aqibu.

     

    Allah ya jiƙan sa da rahma ya gafarta masa. Amiiiin

    Share
  • Innalillahi Wa’inna Ilaihir Raji’un: Allah Ya Yiwa Shahararren Malamin Musulunci A Najeriya Rasuwa Sheikh Dr, Yusuf Ali.

    INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UN 😭

     

    Allah yayiwa shaharraren Malamin Addinin Musulunci da Ɗariƙar Tijjaniyya rasuwa Sheikh Dr. Yusuf Ali a daren jiya, kafin rasuwarsa ya kasance shine Sarkin Malam Gaya, Allah ya masa baiwa iri-iri ga kuma tarin ilimi wanda ya amfani ɗumbin al’umma.

     

    Za’a masa sallah kamar yadda Addinin Muslunci ya tanadar yau Litinin 06/11/2023 da misalin ƙarfe 1:30pm na Rana in Allah ya kaimu a Masallacin Murtala Tudun Maliki.

     

    Allah ya jiƙanshi ya gafarta masa. Amin

     

    Mustapha Abubakar Kwaro

    Tijjaniyya Media News

    Share
  • Innalillah Wa’inna Ilaihir Raji’un: Allah Ya Yiwa Mai Martaba Hakimin Kwadwo Rasuwa Dake Jihar Gombe.

    Innalillahi Wa’inna Ilaihir Raji’un 😭😭

     

    …Masoyin Annabi Muhammadu SAW Ya Rasu.

     

    Allah ya yiwa mai martaba Alhaji Muhammad Sani Abubukar Hakimin Kwadwo rasuwa dake karamar hukumar Yamaltu Deba jihar Gombe.

     

    Muna mika sakon ta’aziyya ga daukacin al’ummar Musulmai musamman masoya Manzon Allah SAW tare da iyalai bisa rasuwa Masoyin mu mai martaba Alhaji Muhammad Sani Abubakar (Hakimin Kwadwo) dake karamar hukumar Yamaltu Deba jihar Gombe.

     

    An gudanar da sallar jana’izan yau talata da misalin karfe 2:00pm na yamma a babban masallacin juma’a na Kwadon dake jihar Gombe.

     

    Allah ya jikan sa da rahma ya gafarta masa, Allah ya karbi shahadar sa. Allah ya yafe masa. Amiiiin Yaa ALLAH.

     

    Tijjaniyya Media News

    Share
  • Inna’lillah Wa’inna Ilaihir Raji’un: Yan Bin@diga Sun Ka@she Mutane Hudu Tare Da Tafiya Da Wasu A Zaria

    ‘Yan Bindi#ga Sun Ka@she Mutane Hudu Tare Da Tafiya Da Wasu A Zaria.

     

    …al’amuran tsa#ro a Arewa na cigaba da tabarbarewa

     

    Rahotanni sun tabbatar da cewa a daren jiya Juma’a da misalin karfe 11na dare , masu gar$kuwa da mutane sun yi dirar mikiya a Anguwan Dankali yankin Dan Magaji dake Zaria.

     

    Maharan sun je gidan Alh Musa, inda suka tafi da mata.

     

    Maha@ran dai sun dinga har@bi ba kakkautawa ga wanda suka yi karo da shi. Inda aka tabbatar da sun kashe mutane hudu tare da ji wa wasu raunuka suna asibiti.

     

    Ya zuwa safiyar nan an samu kiran waya daga matan da aka tafi da su cewa sun kubuta daga hannun masu gar@kuwa da mutanen amma ba su san inda suke ba.

     

    Muna rokon Allah ya jikan wadanda suka rasu.

     

    Ya kubutar da wadanda aka kama, sannan ya yi mana maganin ta’adda@nci da ‘yan ta@’adda.

     

    Daga Abban Al’amin

    Share
Back to top button