RAYUWA

  • FALALA DA SIRRUKAN DA AKE SAMU A CIKIN DAREN NISFU SHA’ABAN

    FALALA DA SIRRUKAN DA AKE SAMU ACIKIN DAREN NISFU SHAABAN

     

    Ita Daren Nisfu Shaaban Dare ce Mai Daraja, Wanda Acikinta ne Allah yake Bononza Na Rahama da Alhairai na Shekara Gaba Daya

     

    Tana Kasancewa ne Ranar 14 ga Wannan Watan Na Sha’aban Da Daddare, (Wato Daren 15 ga Wata)

     

    Anaso Ka Raya Daren Da Ibadu >> Insha Allahu A Post Na Gaba Zamu Kawo Nafilar Da Akeyi Acikin Wannan Daren

     

    Anaso Ka Wayi Gari Da Azumin Bayan Kayi Wancan Nafilar, Allah Zai Sada ka Da Dukkan Alhairan da ake Rabawa

     

    Qissa Mai DaDi Game Da Wannan Dare Da Aka Bamu Mu Alummar Annabi Muhammadu SAW

     

    Wata Rana Annabi Isah Yaga Wani Dutse Yana Haske, Sai Yayi Mamaki, Sai Allah Yace Masa: Kanaso In nuna maka abinda Yafi Wannan Mamaki??

     

    Sai Yace Inaso Ya Ubangiji Sai Allah Ya Umurceshi da ya shiga cikin dutsen, Yana Shiga Sai Yaga Wani Mutum Yana Bautama Allah Aciki Shekaranshi Dari hudu Yana Ibada Bai Taba Fita Ba!

     

    Sai Yace : Ya Ubangiji : Anya Ka Halicci Wani Mutum Da Yayi Maka Bauta Irin Na Wannan Mutumin Kuwa?

     

    Sai Allah Yace: Akwai Wata Dare Wacce Na Baiwa Al umman Masoyina ANNABI MUhammadu S.A.W (Daren Nisfu Shaaban)

     

    A cikinta Duk Wanda Yayi Nafila Raka’a biyu, Zan Bashi Ladan Ibadan Wannan Bawan Allah Da Ya Sami Shekara Dari hudu Yana Bautamin. Allahu Akbar.

    Allah Ka Bamu Ikon Raya Wannan Dare Don Arzikin Annabi Muhammadu SAW. Amiiiin Yaa ALLAH

    Share
  • WADANDA KE TUNAWA DA MUTUWA DA TSAYUWAR HISABI A KOWANNE LOKACI.

    WADANDA KE TUNAWA DA MUTUWA DA TSAYUWAR HISABI A KOWANNE LOKACI.

     

    1- Basu gina dogon buri akan Duniya.

     

    2- Kullum suna cikin neman gafarar ALLAH da yardarsa cikin ayyuka.

     

    3- Suna iya kokarinsu wajen nesantar ha’inta ko cutar da kowaye.

     

    4- Suna kokari tukuru wajen yin ayyukan da zasu amfani lokacinsu da al’umma.

     

    5- Basu hassada ko kyashi cikin wata falala da ALLAH ya huwacewa wani.

     

    6- Suna saurin uzuri da yafiya ga wadanda suka saba musu.

     

    7- Basu neman girma wajen kowa balle tauyewa ya dame su.

     

    8- Suna iya kokarinsu wajen kiyaye neman halal ta hanyar nesantar haramun.

     

    9- Suna takatsa-tsan cikin ababen da suke furtawa saboda hisabin dake gabansu.

     

    10- Ba su girman kai, alfahari, takama, rena halitta ko kuma daukar kawunansu madaukaka akan wasu.

     

    ALLAH KA BAMU IKO MUYI KOYI DA HALAYENSU, KA YAYE MANA GAZAWARMU ALBARKAN ANNABI SALLALLAAHU ALAIHI WASALLAMA

    Share
  • Falalar Watan Sha’aban (Nafiloli Da Kuma Zikirai).

    FALALAN AZUMIN WATAN SHA’ABAN DAGA TASKAR UMAR CHOBBE

     

    ANNABI Muhammadu ﷺ yace wanda yayi azumin Alhamis na farkon watan da Alhamis na karken watan sha aban ’’ Wannan Allah zai shigar dakai Aljanna

     

    Annabi yace duk wanda yayi azumi guda daya acikin watan sha aban

    Allah ya haramta jikinka daga shiga wuta kuma zaka zama makocin annabi yusifa acikin Aljanna Kuma Allah zai baka ladan Annabi ayuba da annabi dawudu

     

    Annabi yace idan kuma kayi azumin watan gaba daya Allah zai sauwakye maka mayan mutuwa Kuma Allah zai tun kude maka duhun kabari kuma zai sauwake maka tan bayan Munkarun da nakiri

     

    Kuma Allah zai sanya maka sutura aranan kiyama randa kowa zai tashi tsirara saidai wasu daga cikin bayinshi wanda yatsabesu

     

    Allah mun gode maka daka zuba mana soyayyar Annabi Muhammadu s,a,w Allah kabiya buka tunmu.

     

    Allah duk wanda yaga rubutunnan yayima annabi salati Allah kasa baya mutuwa sai yaje madina ya ziyarci Annabi Dan girma da martaba da kallan da Allah yayima Annabi afadanshi ran israi da mi iraji

     

    Allah ya karbi ibadun mu albarkan ANNABI S.A.W. Amiiiin Yaa ALLAH

    Share
  • Wani Pastor Igbo Da Membobinsa 3 Suka Karɓi Addinin Musulunci A Garin Lokoja.

    ALHAMDULILLAHI

     

    Musulunci Ya Samu Ƙaruwa; Yayin da Wani Pastor Igbo da Membobinsa 3 Suka Karɓi Addinin Musulunci a Masallaci Anyigba Dake Jihar Kogi. Nan Take Aka Canja Musu Suna.

     

    *Pastor Mike_ Ahmad

    *Samson_Muhammad

    *Ola_Muhummad Mustapha

    *Blessing_Nana Aishatu

     

    Muna Roƙon Allah Yaƙara Ɗaukaka Musulunci da Musulmai a Duk Inda Suke.

     

    ~ ISLAM IN IGBO LAND.

    Share
  • SHARI’A: Mace Tayi Zina Don Ta Samu Abinci Idan Tana Cikin Halin Yunwan Da Zata Iya Mutuwa

    Matsayar Fiqhu Akan Uzuri Ga Mace

     

    Mace tayi zina don ta samu abinci idan tana cikin halin yunwan da za ta iya mutuwa idan ba ta ci abinci ba, da sharhi akan bayanin littafin Mukhtasar da yake cewa:

     

     

    كالمرئة لاتجد ما يسد رمقها إلا لمن يزنى بها

     

     

    …….Inji Sheikh Sani Khalifa Zaria Jihar Kaduna

    Share
Back to top button