TARIHI

  • Shehu Ibrahim Inyass da irin Gudunmawar Daya Bayar Naci Gaban Musulunci a Duniya.

    SHEHU IBRAHIM INYASS YA TAIMAKI MUSULUNCI DA KAYAN ZAMANI

     

    Jama’a assalaumu alaikum, har yanzu dai darasin namu zai ci gaba da tarihin wannan Babban Bawan Allah, Shehu Ibrahim Inyass da irin gudunmawar da ya bayar na ci gaban Musulunci a duniya.

     

    Kamar yadda muka yi bayani a makon da ya gabata, Shehu ya koyar da Sunnar Annabi (SAW) ta tsayar da gemu (tsaka-tsaki) irin yadda Annabi (SAW) yake yi. Ya tilasta wa almajiransa tsayar da gemu har aka san su da shi (gemun) wanda a cikin Malikancin Afirka ba a tsayar da gemu. Hakazalika, ya koyar da almajiransa su riƙa karanta Hadisai musamman Bukhari saboda idan ya kawo musu hukunci kan wani abu su san a ina ya ɗauko musu. Amma a da ba haka ake ba, sai dai a riƙa karanta furu’a (littafan fiƙhu), idan za a faɗi zancen Hadisi; sai dai ka ce leƙa cikin muɗawwalatu za ka gani. Muɗawwalatu a nan suna nufin Hadisai. Ta ɓangaren Ayar Alƙur’ani kuwa, da an ɗan faɗi gutseranta sai a ce karanci ayar da tsawonta ka ji.

    Alherin da Shehin ya koyar a duniyar Musulunci ba su tsaya nan ba.

     

    Shehu Ibrahim ya hori almajiransa da su dinga yin saukar Alƙur’ani a cikin Sallar Tarawihi lokacin Azumin Ramadhan. A wajen almajiran Shehu aka fara ganin haka a Kaulakha. Sannan ya ƙarfafa yin haddar Alƙur’ani mai girma. Albarkar Shehu da kafa makarantun da ya yi, an samu sauƙi sosai wajen yin haddar Alƙur’ani. Bayan haka, Shehu (RA) ya koya mana ‘yancin zaɓi a cikin addini ta yadda kowa zai bi hanyar da yake ganin zai tsira.

     

    Ɓangaren amfani da kayan zamani a addini

    Shehu Ibrahim (RA) ya taimaki addini da kayan zamaninsa da ya tarar wanda Turawan mulkin mallaka suka yi amfani da su. Shi ne farkon Musulmin da ya yi haka. Ya yi amfani da Rediyo, da Tarho, da Rikoda, da Kamara wajen isar da saƙon Musulunci. Don har yau, akwai gidahumin musulmin da yake ganin yin hoto kafirci ne, amma Shehu Ibrahim ne ya wayar mana da kai a kan amfani da waɗannan kayan a cikin addininmu na Musulunci. Haka nan amfani da motoci da jirgin sama, da lasifiƙa, da agogo, da zuwa asibitoci.

     

    Shehu Ibrahim yana daga cikin waɗanda ya tilasta wa almajiransa zuwa asibiti wanda a da ba a yarda da hakan ba. Sannan ya koyar da yin karatu irin wannan da ake yi na zamani a makarantu.

     

    Shehu Ibrahim (RA) shi ne farkon Musulmi kuma Malami da ya waye ya san cewa “technology” ba kishiyar addini ba ne. Shi ne farkon malamin da ya yarda cewa Turawa sun je duniyar wata a shekarar 1969 (combo apolo 11) har ma ya yi littafi a kan wannan. Kuma ya yi wa shugaban Amurka na lokacin wasiƙa a kan wannan (documents suna nan a kan haka). Su Malaman Saudiyya cewa suka yi ma duk wanda ya yarda cewa an je duniyar watan kafiri ne, su kuma na Azahar (Misra) suka ce sam ma ba zai yiwu ba. Amma Shehu Ibrahim ne ya gamsar da su (da hujja) har suka yarda da abin.

    Shehu Ibrahim (RA) ya kewaya ƙasashen duniya har Chana, Beijin, Honkon, da sauran sassan ƙarshen Asiya don taimakon Musulunci. Ya haɗa kan Musulmi Larabawa da Baƙar Fata. Yana da kishi na haƙiƙa a kan addininsa na Musulunci mai tsafta ba na ta’addanci ba.

     

    Shehu Ibrahim (RA) yana da kishi a kan Afirka. Ya yi tsayuwar daka tare da ba da gudummawa ga samun ‘yancin duk wata ƙasa ta Afirka ciki har da ƙasarmu Nijeriya. Yana da kishin mutane baƙar fata ‘yan’uwansa.

     

    Shehu Ibrahim (RA) ne gwarzon namijin da ya tsaya shi kaɗai ya kori Isra’ila daga ƙasarsa Senigal wanda nan ne hanyar shigowa Afirka. A lokacin, Faransa ta yi wa Yahudawa izinin shiga Afirka ta Senigal ba tare da takardar biza ba ma. Ba domin Shehu Ibrahim ya kore su ba da mu ma yanzu abin da yake samun Palasɗinawa ya same mu. Jamilu Arif, wani ɗanjarida na ƙasar Misra ya faɗi wannan.

     

    Da yake duniya ta bunƙasa da kakkafa ƙungiyoyi don cimma abubuwa da dama da aka tasa a gaba, Shehu Ibrahim ya ba da gudummawa ta wannan fuskar don ci gaban Musulunci.

     

    Shehu (RA) ya ba da gagarumar gudummawa wajen kafa Rabiɗa ta Malaman Musulunci na Duniya (duk akwai hujjoji a kai a hannu). Sannan ya kafa haɗin kan Afirka wanda ta hannunsa ne shugabannin Afirka suka karɓi wannan. Ya kuma kafa ƙungiyoyin da za su taimaki addini irin su Ansarid Dini tare da umurtar almajiransa su kafa.

     

    Manyan ‘yan jarida na duniya Turawa da Larabawa da sauran su duk sun yi magana a kan Shehu Ibrahim (RA). Ustazu Abdulkareemin Niyazi ya yi magana a kan Shehu da irin ƙoƙarinsa a Jaridar Saudiyya. Haka nan Jamilu Arif na Misra ya yi magana a kan Shehu. Sannan babban malamin Saudiyya Sheikh Muhammad Mahmud Sauwaf a cikin littafin da ya yi mai suna “Yawona Zuwa ƙasashen Musulunci” ya yi magana a kan Shehu (RA).

     

    Shehu Ibrahim ne malami baƙar fata da ya samu ɗaukakar yi wa Musulmi Sallar Jumma’a a Jami’ar Az’har ta Misra a 1961, wanda kafin shi ba a taɓa yin wannan ba (RA). Haka nan ya riƙe muƙamai da yawa a duniya. Shehu ne na Musulunci wanda yake da fahimtoci a cikin Tauhidi, ya warware abubuwan da ya gagari malamai a cikin Tauhidi cikin sauƙi.

     

    Daga cikin muƙaman da ya riƙe a duniya akwai shugaban haɗin kan Jami’ar ƙairawani da Jami’ar Az’har. Sannan ya riƙe mataimakin taron Musulunci da aka yi a Karachi ta Pakistan. Yana daga cikin kwamitin da ya kafa Rabiɗa ta Malaman Musulunci na duniya a Makka. Sannan yana cikin kwamitin da ya haɗa kan jami’o’in Musulunci na duniya a Ribaɗ na Moroko. Haka nan yana daga cikin babban kwamitin malamai masu yi wa abubuwa hukunci a Musulunci na Misra. Ya riƙe babban matsayi a taron shekara-shekara na bincike a cikin Musulunci a Misra. Har ila yau, yana da matsayi babba a Majalisar Musulunci ta Jaza’ir da sauran su da dama.

     

    Shehu Ibrahim (RA) ya ci nasara wajen yin kira zuwa shiga addinin Musulunci da hikima da wa’azi mai kyau da jayayya mafi kyau. Idan muka ce Musulunci ma’ana ya haɗa da Musuluncin, da Imani da Ihsani kamar yadda Hadisin Annabi (SAW) ya faɗa a Hadisin Jibrilu. Ba a dinga ɗaukar ɓangaren Fiƙhun addini kaɗai a bar sauran ba kamar yadda ta ke faruwa a wannan zamanin, sai mutum ya haɗa duk gaba ɗaya. Amma idan mutum ba zai iya haɗawa ba, ya tsaya wa Fiƙhun addini na maƙamul Islam ɗin kawai amma kuma ya san cewa akwai karatun Imani na ilmud Tauhidi ba adadi a gabansa da bai sani ba, ballantana kuma ilmut Tasawwuf na Ihsani.

     

    Babban makamin Shehu Ibrahim (RT) na wannan aikin shi ne tsoron Allah, da ilimi sannan ya fahimci zamaninsa (wannan nuƙuɗa ce babba). A taƙaice dai kowa ya tabbatar ba a taɓa yin Gwarzon Namiji a Musulunci ba irin Shehu Ibrahim (RA) a ƙarne na 20, ba mu Afirka ba har da ƙasashen Larabawa.

     

    Ya bunƙasa ilimin addini da Luggar Larabci a Afirka wanda duk ga ‘yan jami’a nan suna ta amfani da karatuttukansa. Bayan wannan, ya watsa ‘ya’ya da jikokinsa da almajiransa a ƙasashen Turai suna musuluntar da su tare da karantar da su. Tun komawarsa ga Allah har yau; har abada duk wani abu mai amfani za ka ga imma dai ‘ya’yansa ko jikoki ko almajiransa ne suke jagoranci a kai.

     

    Shehu ya kafa alheri, ya yaɗa alherin amma sai aka zo da kishiyarsa, zuwa da kishiyoyin abubuwan da ya kafa ne ya kai Afirka cikin bala’in da ake ciki.

     

    Rikicin waɗanda ba su fahimci Shehu Ibrahim Inyass ba kawai ya ta’allaƙa ne a kan ƙin tsayawa a matakin ilimin da suke da shi, inda suke kutsawa cikin fannoni ko matakan addini da ba su san komai a kai ba, “suna matakin Fiƙhun Musulunci amma sai su riƙa tsallakawa Matakin Imani na Tauhidi ko Ihsani na Sufanci su riƙa cewa “ya faɗi kaza a wuri kaza” alhali ba su da ilimi a kai ƙwarai da gaske.

     

    Da kowa zai yi adalci ya tsaya a fanninsa sannan ya ɗauki karatun da Shehu Ibrahim ya yi a kan wannan fannin, da ya san Shehu Ibrahim Shehinsa ne don ya karantar da shi a fannin nasa ma.

     

    Haka nan Shehu Ibrahim ya kawar mana da ƙabilanci a tsakaninmu tare da yauƙaƙa zumunci na ‘yan’uwantaka wanda hatta maƙiyinsa ma ya yi masa shaida a kan wannan. Ko a kan haka, ya dace ƙwarai da gaske mu riƙa yin Mauludin Shehu Ibrahim (RA).

    Allah ya saka masa da alkhairi.SHEHU IBRAHIM INYASS YA TAIMAKI MUSULUNCI DA KAYAN ZAMANI

     

    Jama’a assalaumu alaikum, har yanzu dai darasin namu zai ci gaba da tarihin wannan Babban Bawan Allah, Shehu Ibrahim Inyass da irin gudunmawar da ya bayar na ci gaban Musulunci a duniya.

     

    Kamar yadda muka yi bayani a makon da ya gabata, Shehu ya koyar da Sunnar Annabi (SAW) ta tsayar da gemu (tsaka-tsaki) irin yadda Annabi (SAW) yake yi. Ya tilasta wa almajiransa tsayar da gemu har aka san su da shi (gemun) wanda a cikin Malikancin Afirka ba a tsayar da gemu. Hakazalika, ya koyar da almajiransa su riƙa karanta Hadisai musamman Bukhari saboda idan ya kawo musu hukunci kan wani abu su san a ina ya ɗauko musu. Amma a da ba haka ake ba, sai dai a riƙa karanta furu’a (littafan fiƙhu), idan za a faɗi zancen Hadisi; sai dai ka ce leƙa cikin muɗawwalatu za ka gani. Muɗawwalatu a nan suna nufin Hadisai. Ta ɓangaren Ayar Alƙur’ani kuwa, da an ɗan faɗi gutseranta sai a ce karanci ayar da tsawonta ka ji.

    Alherin da Shehin ya koyar a duniyar Musulunci ba su tsaya nan ba.

     

    Shehu Ibrahim ya hori almajiransa da su dinga yin saukar Alƙur’ani a cikin Sallar Tarawihi lokacin Azumin Ramadhan. A wajen almajiran Shehu aka fara ganin haka a Kaulakha. Sannan ya ƙarfafa yin haddar Alƙur’ani mai girma. Albarkar Shehu da kafa makarantun da ya yi, an samu sauƙi sosai wajen yin haddar Alƙur’ani. Bayan haka, Shehu (RA) ya koya mana ‘yancin zaɓi a cikin addini ta yadda kowa zai bi hanyar da yake ganin zai tsira.

     

    Ɓangaren amfani da kayan zamani a addini

    Shehu Ibrahim (RA) ya taimaki addini da kayan zamaninsa da ya tarar wanda Turawan mulkin mallaka suka yi amfani da su. Shi ne farkon Musulmin da ya yi haka. Ya yi amfani da Rediyo, da Tarho, da Rikoda, da Kamara wajen isar da saƙon Musulunci. Don har yau, akwai gidahumin musulmin da yake ganin yin hoto kafirci ne, amma Shehu Ibrahim ne ya wayar mana da kai a kan amfani da waɗannan kayan a cikin addininmu na Musulunci. Haka nan amfani da motoci da jirgin sama, da lasifiƙa, da agogo, da zuwa asibitoci.

     

    Shehu Ibrahim yana daga cikin waɗanda ya tilasta wa almajiransa zuwa asibiti wanda a da ba a yarda da hakan ba. Sannan ya koyar da yin karatu irin wannan da ake yi na zamani a makarantu.

     

    Shehu Ibrahim (RA) shi ne farkon Musulmi kuma Malami da ya waye ya san cewa “technology” ba kishiyar addini ba ne. Shi ne farkon malamin da ya yarda cewa Turawa sun je duniyar wata a shekarar 1969 (combo apolo 11) har ma ya yi littafi a kan wannan. Kuma ya yi wa shugaban Amurka na lokacin wasiƙa a kan wannan (documents suna nan a kan haka). Su Malaman Saudiyya cewa suka yi ma duk wanda ya yarda cewa an je duniyar watan kafiri ne, su kuma na Azahar (Misra) suka ce sam ma ba zai yiwu ba. Amma Shehu Ibrahim ne ya gamsar da su (da hujja) har suka yarda da abin.

    Shehu Ibrahim (RA) ya kewaya ƙasashen duniya har Chana, Beijin, Honkon, da sauran sassan ƙarshen Asiya don taimakon Musulunci. Ya haɗa kan Musulmi Larabawa da Baƙar Fata. Yana da kishi na haƙiƙa a kan addininsa na Musulunci mai tsafta ba na ta’addanci ba.

     

    Shehu Ibrahim (RA) yana da kishi a kan Afirka. Ya yi tsayuwar daka tare da ba da gudummawa ga samun ‘yancin duk wata ƙasa ta Afirka ciki har da ƙasarmu Nijeriya. Yana da kishin mutane baƙar fata ‘yan’uwansa.

     

    Shehu Ibrahim (RA) ne gwarzon namijin da ya tsaya shi kaɗai ya kori Isra’ila daga ƙasarsa Senigal wanda nan ne hanyar shigowa Afirka. A lokacin, Faransa ta yi wa Yahudawa izinin shiga Afirka ta Senigal ba tare da takardar biza ba ma. Ba domin Shehu Ibrahim ya kore su ba da mu ma yanzu abin da yake samun Palasɗinawa ya same mu. Jamilu Arif, wani ɗanjarida na ƙasar Misra ya faɗi wannan.

     

    Da yake duniya ta bunƙasa da kakkafa ƙungiyoyi don cimma abubuwa da dama da aka tasa a gaba, Shehu Ibrahim ya ba da gudummawa ta wannan fuskar don ci gaban Musulunci.

     

    Shehu (RA) ya ba da gagarumar gudummawa wajen kafa Rabiɗa ta Malaman Musulunci na Duniya (duk akwai hujjoji a kai a hannu). Sannan ya kafa haɗin kan Afirka wanda ta hannunsa ne shugabannin Afirka suka karɓi wannan. Ya kuma kafa ƙungiyoyin da za su taimaki addini irin su Ansarid Dini tare da umurtar almajiransa su kafa.

     

    Manyan ‘yan jarida na duniya Turawa da Larabawa da sauran su duk sun yi magana a kan Shehu Ibrahim (RA). Ustazu Abdulkareemin Niyazi ya yi magana a kan Shehu da irin ƙoƙarinsa a Jaridar Saudiyya. Haka nan Jamilu Arif na Misra ya yi magana a kan Shehu. Sannan babban malamin Saudiyya Sheikh Muhammad Mahmud Sauwaf a cikin littafin da ya yi mai suna “Yawona Zuwa ƙasashen Musulunci” ya yi magana a kan Shehu (RA).

     

    Shehu Ibrahim ne malami baƙar fata da ya samu ɗaukakar yi wa Musulmi Sallar Jumma’a a Jami’ar Az’har ta Misra a 1961, wanda kafin shi ba a taɓa yin wannan ba (RA). Haka nan ya riƙe muƙamai da yawa a duniya. Shehu ne na Musulunci wanda yake da fahimtoci a cikin Tauhidi, ya warware abubuwan da ya gagari malamai a cikin Tauhidi cikin sauƙi.

     

    Daga cikin muƙaman da ya riƙe a duniya akwai shugaban haɗin kan Jami’ar ƙairawani da Jami’ar Az’har. Sannan ya riƙe mataimakin taron Musulunci da aka yi a Karachi ta Pakistan. Yana daga cikin kwamitin da ya kafa Rabiɗa ta Malaman Musulunci na duniya a Makka. Sannan yana cikin kwamitin da ya haɗa kan jami’o’in Musulunci na duniya a Ribaɗ na Moroko. Haka nan yana daga cikin babban kwamitin malamai masu yi wa abubuwa hukunci a Musulunci na Misra. Ya riƙe babban matsayi a taron shekara-shekara na bincike a cikin Musulunci a Misra. Har ila yau, yana da matsayi babba a Majalisar Musulunci ta Jaza’ir da sauran su da dama.

     

    Shehu Ibrahim (RA) ya ci nasara wajen yin kira zuwa shiga addinin Musulunci da hikima da wa’azi mai kyau da jayayya mafi kyau. Idan muka ce Musulunci ma’ana ya haɗa da Musuluncin, da Imani da Ihsani kamar yadda Hadisin Annabi (SAW) ya faɗa a Hadisin Jibrilu. Ba a dinga ɗaukar ɓangaren Fiƙhun addini kaɗai a bar sauran ba kamar yadda ta ke faruwa a wannan zamanin, sai mutum ya haɗa duk gaba ɗaya. Amma idan mutum ba zai iya haɗawa ba, ya tsaya wa Fiƙhun addini na maƙamul Islam ɗin kawai amma kuma ya san cewa akwai karatun Imani na ilmud Tauhidi ba adadi a gabansa da bai sani ba, ballantana kuma ilmut Tasawwuf na Ihsani.

     

    Babban makamin Shehu Ibrahim (RT) na wannan aikin shi ne tsoron Allah, da ilimi sannan ya fahimci zamaninsa (wannan nuƙuɗa ce babba). A taƙaice dai kowa ya tabbatar ba a taɓa yin Gwarzon Namiji a Musulunci ba irin Shehu Ibrahim (RA) a ƙarne na 20, ba mu Afirka ba har da ƙasashen Larabawa.

     

    Ya bunƙasa ilimin addini da Luggar Larabci a Afirka wanda duk ga ‘yan jami’a nan suna ta amfani da karatuttukansa. Bayan wannan, ya watsa ‘ya’ya da jikokinsa da almajiransa a ƙasashen Turai suna musuluntar da su tare da karantar da su. Tun komawarsa ga Allah har yau; har abada duk wani abu mai amfani za ka ga imma dai ‘ya’yansa ko jikoki ko almajiransa ne suke jagoranci a kai.

     

    Shehu ya kafa alheri, ya yaɗa alherin amma sai aka zo da kishiyarsa, zuwa da kishiyoyin abubuwan da ya kafa ne ya kai Afirka cikin bala’in da ake ciki.

     

    Rikicin waɗanda ba su fahimci Shehu Ibrahim Inyass ba kawai ya ta’allaƙa ne a kan ƙin tsayawa a matakin ilimin da suke da shi, inda suke kutsawa cikin fannoni ko matakan addini da ba su san komai a kai ba, “suna matakin Fiƙhun Musulunci amma sai su riƙa tsallakawa Matakin Imani na Tauhidi ko Ihsani na Sufanci su riƙa cewa “ya faɗi kaza a wuri kaza” alhali ba su da ilimi a kai ƙwarai da gaske.

     

    Da kowa zai yi adalci ya tsaya a fanninsa sannan ya ɗauki karatun da Shehu Ibrahim ya yi a kan wannan fannin, da ya san Shehu Ibrahim Shehinsa ne don ya karantar da shi a fannin nasa ma.

     

    Haka nan Shehu Ibrahim ya kawar mana da ƙabilanci a tsakaninmu tare da yauƙaƙa zumunci na ‘yan’uwantaka wanda hatta maƙiyinsa ma ya yi masa shaida a kan wannan. Ko a kan haka, ya dace ƙwarai da gaske mu riƙa yin Mauludin Shehu Ibrahim (RA).

     

    Allah ya saka masa da alkhairi. Amiiiin

     

    Sheikh isma’ila umar almaddah r.a.

     

    Sabi’u Hashim Hassan Al-tijany

    Sheikh khaleell zawiyyah Bauchi

    Asabar-25/11/2023

    Share
  • Tarihin Imam Ahmad Ibn Hambal Rayuwarsa Da Gudumawar Sa Akan Addinin Musulunci.

    Tarihin Imam Ahmad Ibn Hambal. ( Ahmad ibn Hanbal al-Dhuhli ) أَحْمَد بْن حَنْبَل الذهلي.

     

    IMAMU AHMAD IBN HAMBAL

     

     

    Ahmad ibn Hanbal al-Dhuhli, masanin shari’a musulmi ne, masanin tauhidi, mai kishin addini, masanin hadisi, kuma wanda ya assasa mazhabar Hanbali ta fikihun Sunna – daya daga cikin manyan mazhabobin shari’a guda hudu na Ahlus-Sunnah.

     

    Haihuwa: 164 AH Wanda Yazo Dai-Dai Da, 780 miladiyya

     

    An Haifeshi a Baghdad babban birnin kasar Iraki ne kuma birni na biyu mafi girma a kasashen Larabawa bayan Alkahira. Tana kan Tigris kusa da kango na tsohon birnin Akkadiya na Babila da kuma babban birnin Farisa na Sassanid na Ctesiphon.

     

    MATSAYI: IMAMU AHLUS SUNNAH

     

    Mutuwa: 241 AH

     

    Ibn Hanbal ya rasu a ranar Juma’a 12 Rabi’ul-awwal, 241H/ 2 August, 855 yana da shekaru 74-75 a birnin Bagadaza na kasar Iraki. Masana tarihi sun bayyana cewa a ranar jana’izar sa ya samu halartar mazaje 800,000 da mata 60,000 kuma a wannan rana Kiristoci da Yahudawa dubu 20 ne suka musulunta

     

    NASABA

     

    Shi ne Ahmad Ibn Hambal Ibn Hilal Ibn Asad Ibn Idrees Ibn Abdullah Ibn Hayyan Ibn Abdullah Ibn Anas Ibn Auf Ibn Qasit Ibn Maazin Ibn Shayban Ibn Zahl Ibn Sa’alaba Ibn Ukaba Ibn Sa’ab Ibn Aliy Ibn Bakr Ibn Wa’il, Imam Abu Abdullah As Shayban, kamar yadda dansa Abdullahi ya nasabta shi.

     

    NEMAN ILMI

     

    Kadibul Bagdadi ya ce, an haifi Abu Abdullahi a Bagdaza, ya nemi ilmi a cikinta, sannan sai ya fita zuwa Kufa da Basra da Makka da Madina da Yamen da Sham da Jazira.

     

    Imamu Ahmad ya haddace hadisai miliyan guda. Amma aka ce hadisan daga ma’aikin Allah ba su kai wannan adadin ba, saboda haka ana ganin ya hada da maganganun Sahabbai ne da Tabi’ai.

     

     

    MALAMAI

     

    Daga cikin fitattun Malaman da ya yi karatu a wajensu akwai, Hushaimu da Abdur Razak da Sufyanu Ibn Uyayna da Waki’u da Imamus Shafi’i da sauransu.

     

    DALIBAI

     

    Imamul Bukhari da Muslim da Abu Dauda sun ruwaici hadisai daga gare shi babu shamaki. Tirmizi da Nasa’i da Ibn Majah kuwa sun ruwaito daga gare shi amma da shamaki. ‘Ya’yansa guda biyu, Salihu da Abdullahi sun ruwaito daga gare shi. Malaminsa ma Imamus Shafi’i ya ruwaito daga gare shi.

     

    Abu Dauda ya ce, majalisin Ahmad ta kasance majalisi ne na lahira, ba ya ambaton komai na duniya, ban taba ji ya ambaci duniya ba.

     

    TSANTSENI

     

    Imamu Ahmad yana da tsantseni sosai. Ya kasance ko kyauta ba ya karba a hannun mutane musamman ma masu mulki. Yana da tsananin bibiyar sunnah da kyamar bid’a.

     

    GWAGWARMAYA

     

    Imamu Ahmad ya sha gwagwarmaya sosai wajen fada da Akidar nan ta halittar Alkur’ani Mu’utazilawa da Jahamiyawa suka fara kirkiro da wannan bidi’ar a zamanin Rashid. Bayan da Ma’amun ya hau mulki ya yarda da wannan ra’ayin inda ya fara kama malamai da suke inkarin wannan ra’ayi cikinsu har da Imamu Ahmad.

     

    Imamu Ahmad ya kasance a daure cikin sarka har zuwa lokacin Mu’utasim. An ci gaba da tsare shi ana kawo shi gaban Mu’utasim don ya yarda da wannan karkataccen ra’ayi amma ya ki yarda, aka yi ta masa bulalu amma yaki ba da gari. Haka a ka yi ta azabtar da Imamu Ahmad na tsawan shekaru biyu da wata hudu amma bai canza maganarsa ba har aka hakura aka sake shi.

     

    Bayan Mutuwar Mu’utasim, Alwasik ya zama Kalifa Imamu Ahmad ya warke daga raunukan da aka ji masa. Alwasik shi ma ya ci gaba da takun-saka da Imamu Ahmad.

     

    Bayan mutuwar Alwasik, Mutawakkil ya zama Kalifa. Daga bisani ya dauke Imamu Ahmad daga Bagdaza har aka yi masa daurin talala a Askar.

     

    Mutawwakkil ya yi kokarin kyayratawa Imamu Ahmad amma ba ya karba kyautarsa da ma abincinsa. Haka ya ci gaba da rayuwa cikin yunwa da Azimi.

     

    Daga karshe an yi masa izinin komawa garin Bagdaza.

     

    Wani Malami Ibrahim alharbi a zamanin yake cewa, ban taba ganin mutumin da Allah ya tara masa imin mutanan farko da na karshe ba kamar Imam Ahmad, ana yi masa lakabi da imam Ahlussunnah saboda jajircewarsa da tsananin riko da Sunnah lokacin fitinar: cewa kur’ani makhluq ne, wanda imam Ahmad ya tsaya a kan cewa kur’ani zancen Allah ne kuma ba makhluq ba ne.

     

    Imam kutaiba yana cewa: mafi alkhairin mutane a zamaninmu shine: Ibn Mubarak sannan wannan saurayin, wato Imam Ahmad bin Hanbal, idan ka ga mutum yana son imam Ahmad to ka tabbatar cewa wannan mutumin Ahlussunnah ne

     

    MUTUWA

     

    Imamu Ahmad ya kamu da rashin lafiya laraba biyu ga watan Rabi’ul Auwal, ya shafe kwana tara yana jinya. Ranar Juma’a 12 ga watan ya bar duniya yana da shekaru 77 a duniya a shekara ta 241 bayan hijira rahimahullah.

    Share
  • Bikin Takutaha A Kano Ya Cika Shekaru 700 Da Fara Gudanarwa.

    Bikin Takutaha A Kano ya cika Shekaru 700 biki ne na murnar yin nasarar rushe tsunburbura da yai dai dai da ranar Sunan manzon Allah Sallallahu Alaihiwasallam.

     

    ASALIN BIKIN TAKUTAHA A KANO

     

    TUN DAGA ZAMANIN SARKIN KANO ALI YAJI DAN TSAMIYA.

     

    A duk 19 ga watan Rabiul Awwal, a jihar Kano kanawa suna gudanar da wani bikin Wanda ake Kira Takutaha.

     

    Shin menene Asalin Tarihin sa ? Menene Alakar Bikin da Addinin musulunci ?

     

    A wata shekara zamanin sarkin Kano Yaji dan Tsamiya, wasu malaman Wangarawa karkashin jagorancin sheikh AbdurRahman Zaiti suka zo, Kano, baya ga musulunci da kuma kasuwanci, suna da dabarun yaki da baa san da su ba a Kano. Bagaudawa suka karbi musulunci, hannun su, su kuma su taimaka musu don su yaki abokan gabarsu. Kwana daya da zuwansu Sarkin Kano Yaji ya karbi musulunci, ya kuma canjawa kansa suna zuwa Ali. Wanda hakan ke nuna, cewa , shirin yaki zaayi, domin ana cewa Ali bin Abu Talib shine sarkin yakin manzon Allah (saw). Kafin Ali yaji ya musulunta akwai musulmai a Kano saidai basu kai ga kafa mulki ba

     

    A farkon watan Rabiul Awwal na wannan shekara, ne Yaji ya tara dukkan maguzawa, ya kuma karanta musu dokar-ta-baci. Inda yace musu

     

    “Ku sani, daga yau, komai tsakanina daku, sai yaki da tsinin mashi, ba yaudara, bawani boye boye, domin ba mayaudari sai matsoraci, ku shirya gani nan zuwa gareku ko ku karɓi Addinin Musulunci kafin lokacin anyi masu wa’azi suka butulce”

     

    Mataki biyu suka dauka, na farko sunyi kokarin bada cin hanci ga Sarki Yaji, amma yaki karba, yace a maida musu baya so. Na biyu, sai suka koma ga Tsumburbura, domin neman nasara, amma ta gaya musu, cewa wannan yaki ba nasara, domin lokacin karshen addininsu a kasar Kano yazo.

     

    Acikin watan dai, rundunar musulmi suka fuskanci, rundunar maguzawa, a gefen Dutsen Dala, inda suka hadu, aka gwabza. A wannan lokacin ne, Jarmai Bajere ya samu nasarar Kutsa kai cikin shigifar Tsumburbura, inda ya samu wani halitta na tsaye, rike da maciji a hannunsa, ya daga mashi ya bugawa halittar nan, tayi kuwwa ta fito a guje. Nan da nan suka bita, inda ta nufi kofar ruwa, ta fada cikin ruwan Dankwai. Wannan Shi ya kawo karshen Tsumburbura, da kuma addinin maguzawa a garin Kano.

     

    Samuwar wannan Nasara, ba karamin abu bane a wurin musulman Kano. Wanda aka shafe sama da shekaru 100 ana nema. A dalilin haka ne, ya sanya musulman kanawa duk shekara, sukan taru su hau Dutsen Dala domin tunawa da wannan nasara da musulunci yayi akan Maguzanci. Su nunawa duniya cewa, addinin Allah yau ya shafe addinin kafirai. Domin kafin zuwan musulunci, ba mai hawa Dala in ba Babban limamin addinin ba. Amma zuwan musulunci, yanzu kowa ma sai ya hau, ya yi kashi ma aka. Wannan shine dalilin da ya sanya ake takutaha a duk shekara a Kano.

     

    MENENE MA’ANAR KALMAR TAKUTAHA ?

     

    An sha kai-kawo a tsakanin masana game da ma’ana ko asalin wannan kalma ta takutaha. Wannan ce ta sa aka sami mabambantan ra’ayoyi game da wannan kalma.

     

    Daga ciki akwai Hassan (1998:94) ya nuna cewa, bayan al’ummar Kano sun rungumi wannan rana ne ta takutaha, sai Maguzawa da suke gabatar da bukukuwansu na bauta a lokacin suka damu, wasu suka bar garin zuwa qauyuka, suna cewa, “wannan sallar taku-ta ba tamu ba ce”. Daga nan sai aka sami kalmar takutaha.

     

    Wasu kuwa suna ganin Kalmar ta samu ne daga qaulin Shehu Usmanu Danfodiyo, a lokacin da almajiransa suka yiyo bara a ranar da shekarar da aka haifi Annabi salallahu alaihi wasallam ta kewayo, amma sai ya qi daukar komai a ciki, ya ce, “ ai wannan taku ta”. Daga nan sai aka sami kalmar “takutaha”.

     

    Wasu kuma suna ganin ma’anar Kalmar takutaha ita ce, “Allah ya maimaita mana”, wasu kuma sun ce sunan Ma’aiki ne. Haka nan, wasu suna ganin Kalmar ta samu ne daga sunan wata baiwar Allah mai suna Taku, ‘yar Malam Usman Attuman, babban waliyin nan da ya zauna a Madabo.

     

    A dunqule, za a iya cewa bikin takutaha yana daya daga cikin bukukuwan addini da ake yin sa a birnin Kano, duk ranar 19 ga watan Rabi’ul awwal, wato watan da aka haifi Annabi Muhammadu salallahu alaihi wasallam kuma dai-dai da ranar sunan sa.

    Share
  • TAKAITACCEN TARIHIN MAULANMU SHEIKH MODIBBO ALIYU JOBBO GOMBE

    {TAƘAITACHCHEN TARIHIN MAULANMU SHEIKH MODIBBO ALIYU JOBBO GOMBE}

     

    Sunan Sa Modibbo Aliyu, Amma Anfi Sanin Sa Da {Modibbo Joɓɓo} Dan Modibbo Abbdullahi (Shetiman Dukku) Dan Modibbo Ardo Haruna Jikan Modibbo Ardo Sambo Bodejo, Wato Sarkin Fulani Na farko A kasar Dukku, Sunzo Ƙasar Dukku Tun Kafin Jihadin Shehu Usman Dan-Fodiyo A Shekara Ta 1804.

     

    Kamar Yanda Yazo A Tarihi, Sunzo Ne Daga Yammacin Kasar Sudan Wato Yankin {Kurdufan} Sun Biyo Yankin {Kanem Borno} Har Suka Tsaya A {Qatar Kalam} Wato Dukku A Yanzu, Inda Wasunsu Kuma Suka Wuche Garin Jama’are Dakuma Garin Shira, Wanda Duk Waɗannan Garuruwan Suke A Jahar Bauchi, Sannan Akwai Wadanda Suka Wuche Chan Garin {Jahun} Dake Jahar Jigawa.

     

    {MAHAIFAR SA}

     

    An Haifi Maulanmu Modibbo Jobbo A Garin Dukku Dake Jahar Gombe, An Haifeshi A Tsakanin Shekara (1895) Kokuma (1898) Inda Ya Rayu Tsawon Shekaru 78 Kokuma (81) Domin Yayi Wafati A Shekara Ta (1973).

     

    {RAYUWAR SA}

     

    Shehu Modibbo Ya Rayu Chikin Tarbiyya Ta Ƙwarai Wanda Ya Gajeta A Wajen Mahaifansa Wato {Modibbo Abdullahi} Da Kuma {Sayyada Fadimatu} Wato Mahaifiyar Sa.

     

    Shehu Ya’ Fa’ra Karatun Addini A Gaban Mahaifansa, Yayi Karatun Al-ƙur’ani A Makarantar Mahaifinsa Sannan Kuma Ya Fara Da Kararun Littatafai A Wajen Mahaifin Sa.

     

    Daga Nan Sai Shehi Ya Chigaba Da Zama A Wajan Wan Mahaifinsa, Wato Sarkin Dukku Na Wanchan Lokacin {Sarki Haruna Rashid} Ya Koma Hannun Wan Mahaifinsa Ne Kasanche War An Tura Mahaifinsa Zuwa Wani Babban Yanki Domin Ya Chigaba Da Karantar Da Al’ummar Wajen Addinin Allah S.w.t. Kamar Yadda Suka Gada (Karantarwa)

     

    Modibbo Ya Zauna A Dukku Baibi Mahaifinsa Ba, Domin Kuwa Sarki Haruna Rashidi Yache “Yana Son Zama Dashi” Sirrin Hakan Kuwa Shine: Watarana Anyi Wani Bakon Babban Malam Da Hanya Ta Biyo Dashi Garin Ya’zo Wuche Wa, Ya Nuna Shehu Yache “Wannan Yaro Zai Taka Matsayi Mai Girma A Wulaya”

     

    Daga Zaman Modibbo Jobbo A Garin Dukku Kuma, Sai Ya Nausa Garin Gombe Wajen Wani Babban Malami Kuma Alkalin Gari Sannan Kuma Wazirin Gari Wato {Shehu Ahmad Tijjani bn Abubakar} Wanda Maulanmu Sheikhul Islam Alhaji Ibrahim Inyass R.t.a. Yake Yabonsa A Rihla Hijaziyyah.

     

    Shehu Modibbo Yayi Karatu Tukuru Inda Har Yakai Matsayinda Babu Kamar Sa Aduk Abokan Karatunsa Wanda Har Malamin Sa Dakansa Yake Chewa “Duk Wanda Yayi Karatu A Wajena, To Ya Maimaita A Wajen Modibbo Jobbo” Wanda Kuma Sau Da Yawa Yakan Fada Musu “Kudinga Daukan Karatu A Wajensa” {Modibbo Jobbo}

     

    An Fada Chewa, Irin Wannan Makaranta Ta Waziri Tijjani A Wanchan Lokachin, Babu Inda Ake Samun Kamarta A Kasar Nan, Sai Kaje Garin Kano Ko Kuma Birnin Zariya.

     

    {KADAN DAGA CHIKIN DALIBAN MAKARANTAR}

     

    *Modibbo Jailani Yola*

    *Modibbo Umar Jarkasa*

    *Modibbo Tukur Gombe*

    *Modibbo Muhammad Kagadama* {Jigawa

    *Shehu Manzo Gombe*

    *Modibbo Ali Gombejo*

     

    👆Da Sauransu👆

     

    Akwai Manyan Malamai Sama Da Malamai Dari Uku 300 Da Sukayi Karatu A Wannan Makaranta, Wanda Wasu Sun Fito Ne Daga Kasashe Kamar Irinsu Nigeria, Nijar, Kamaru, Central Africa Da Sauran Su.

     

    {BAYAN WAFATIN WAZIRI TIJJANI}

     

    Waziri Tijjani Yayi Wafati A Garin Makka Bayan Komawar Sa Aikin Hajji Inda Bayan Wafatinsa Sai Almajiransa {Waziri Tijjani} Gaba Dayansu Suka Dawo Wajen Modibbo Jobbo Da Karatu, Inda Ya Zamto Babban Malami Kuma Jagora Ga Dukkan Almajiran Maulanmu Shehu Ibrahim Inyass R.t.a. Dake Garin Gombe Da Kewaye, Inda Zawiyyar Sa Kuma Ta Zamo Head Quarter Faila Bayan Bayyanar Faidar Shehu Ibrahim.

     

    Modibbo Joɓɓo Yakai Matsayin Da Duk Wani Abunda Maulanmu Shehu Ibrahim Zai Aikowa Mutanen Gombe Daga Madinatu Kaulaha Zuwa Ga Shehunnai Da Muqaddamai Da Muridai Dake Jahar Gombe Da Kewaye, Shi Yake Aikowa Direct, Domin Akwai Alaqa Sosai Tsakanin Sa Da Shehu Ibrahim.

     

    {IJAZA}

     

    Modibbo Jobbo Yanada Ijazozi Daban Daban Daga Shehunai Mabanbanta Kamar Irinsu Shehinsa Shehu Waziri Tijjani,

     

    *Sheikh Bn Umar Ainamali*

    *Sheikh Adamu Badamagare Azare*

    *Shekhul Hadith, Sheikh Isma’il Bn Ali {Makkatul Mukarram}

    *Sheikhul Hadi Murtania*

    *Sheikh Ibrahim Inyass (R.A).

     

    {ALMAJIRAN SA}

     

    Sheikh Modibbo Jobbo Yanada Almajirai Da Dama Kamar Yadda Muka Fada A Baya, Inda Kusan Dukkan Almajiran Waziri Tijjani {Malamin Sa} Almajiransane.

     

    Saidai Ga Jerin Sunayen Wasu Daga Chikin Almajiransa Da Sukayi Fiche. 👇

     

    *Shehu Dahiru Usman Bauchi (R.A)

    *Shehu Manzo Gombe (R.A)

    *Shehu Modibbo Tukur Gombe (R.A)

    *Shehu Ibrahim Bogo (R.A)

    *Shehu Modibbo Muhammad Ali Garuza (R.A)

    *Grand Khadi Yahya Ahmad (R.A)

    *Sheikh Bashir Modibbo Jobbo (R.A) {Khalifa}

    *Sayyidi Habibu Modibbo Jobbo (R.A) *Modibbo Jelani Yola (R.A) Wanda Shekarun Sa Biyu A Zawiyar Modibbo jobbo)

     

    {MATAN SA}

     

    *Sayyada Dudu*

    *Sayyada Fadimatu*

    *Sayyada Aishatu*

    *Sayyada Fadimatu*

     

    {YA’YA’NSA}

     

    Sheikh Modibbo Jobbo Yanada Ya’ya Takwas, Maza Hudu Mata Hudu.

     

    {MAZA}

     

    *Sheikh Bashir Modibbo Jobbo*

    *Sheikh Habibu*

    *Sayyidi Mustapha*

    *Sayyidi Ahmad Tijjani*

     

    {MATA}

     

    *Sayyada Balkisu*

    *Sayyada Asma’u*

    *Sayyada Rukayya*

    *Sayyada Rabi’atu*

     

    {BAYAN WAFATINSA}

     

    Khalifah Sheikh Bashir Modibbo Shine Ya Chigaba Da Khalifan Chi Game Da Kuma Jagoranci Na Zawiyyar Sa Wajen Chigaba Da Bada Ilimi, Tarbiya Ta Zahiri Da Badini Bayan Wafatinsa A Shekara Ta (1973).

     

    {INDA ZAWIYAR TAKE}

     

    Zawiyar Tana Nan Akan Titin Jankai, Yamma Da {Gombe Division} Gabar Da Zawiyyar Sheikh Modibbo Tukur Gombe.

     

    Allah Kabamu Albarkacin Sa Da Zuri’ar Sa

     

    ✍️ Adamu Habibu Jobbo

    📝 Muhammad Izzuddin Abubakar

    Share
  • Garin Tabuk Wanda Allah Ya Albarkaci Garin Da Kayan Lambu Saboda Addu’an Manzon Allah SAW.

    Garin Tabuk yana daga cikin mu’ujjizan Manzon Allah Saww ﷺ.

     

    Lokacin da Annabi ya tafi yaki sun tsaya a garin Tabuk wanda yake da ruwa kaɗan – sai ya wanke fuskarsa da hannayensa masu daraja sannan ya zuba ruwan a cikin kayan marmari sannan ya ce, ‘Ya Mu’azu, wataƙila idan ka yi tsawon rai, da sannu za ka ga wannan yanki cike da lambuna.

     

    Albarkar Annabi Muhammadu Saww, a kwana a tashi a yanzu ana fitar da sama da wardi miliyan 20 a duk duniya daga Tabuk kowace shekara.

     

    Bayan haka, garin cike yake da lambuna masu albarka, ƙasa mai albarka, da ‘ya’yan itatuwa da kayan marmari masu yawa. Tabuk yana daya daga cikin wuraren aikin gona a duk yankin kasar Saudi Arabia.

     

    Allah ya kara masa soyayyan Manzon Allah Saww, ﷺ. Amiin Yaa ALLAH.

     

    Daga: Babangida A. Maina

    Share
Back to top button