TARIHIN ANNABI

  • TARIHIN MANZON ALLAH ANNABI MUHAMMADU SAW KASHI NA TALATIN DA DAYA (31)

    TARIHIN ANNABI MUHAMMAD (SAW) Kashi na 31

     

    WAFATIN ANNABI MUHAMMAD (SAW)

     

    Daga: Muhammad Yaseen Bin Hussain

     

    Annabi Muhammad (SAW) yayi Wafati bayan Jinya da yayi fama da ita. Da Jin Labarin Wafatin Annabi Muhammad (SAW), Sahabbai sukayi dafifi a Kofar gidansa domin Hali da suka Shiga na Jimami inda wasu daga cikinsu Basu yarda akan cewa yayi Wafati ba.

     

    Sayyidina Umar (RTA) na cikin Wadanda Basu yarda cewa Annabi Muhammad (SAW) yayi Wafati ba a wannan lokacin. Dajin labarin Wafatin Annabi Muhammad (SAW), ya fitar da takobinsa cewa sai ya sare kan duk wanda kecewa Annabi Muhammad (SAW) yayi Wafati mutane su daina faɗan haka karya suke (shin Sayyidina Umar bai yarda ba)

     

    A Wannan Lokaci Sayyidina Abubakar baya kusa. Amma dajin labarin Wafatin Annabi Muhammad (SAW), sai ya garzayo izuwa Gidan Annabi Muhammad (SAW) domin ya tabbatar. Dazuwansa Ya Shiga Gidan Annabi Muhammad (SAW) ya tabbatar da Wafatin nasa yayi kuka kwarai da gaske domin Rashin Masoyinsa, sai ya fito waje domin yayiwa Al’ummah jawabi.

     

    Da fitowarsa ya hau kan minbari, yayi jawabi; ga kadan daga cikin Jawabinsa: Sayyidina Abubakar yace “Lallai wanda yakasance Annabi Muhammad (SAW) yake bautawa to Hakika Annabi Muhammad (SAW) yayi Wafati, Wanda yakasance yana bautawa Allah (SWT) ne kuma, to Allah Rayayye ne baya Mutuwa. Ya karanta wannan Ayar daga Alqur’ani Maigirma _’Annabi Muhammadu baikasance ba sai dai Annabi da Annabawa suka wuce kafinsa, Idan yayi Wafati ko aka kasheshi sai kujuya baya zuwa ga Kafurcinku nada, Wanda ya juya baya bazai cutar Allah da komai ba, da sannu Allah zai sakawa Masu gode masa'”_.

     

    Annabi Muhammad (SAW) yayi Wafati ranar Litinin 12 ga watan Rabi’ul Auwal Shekara ta 11 bayan Hijira. Yayi Wafati yanda Shekara 63.

     

    Alqawarin Allah ne dukkan Mai rai za’a wayi gari watarana babu shi, mu mun yarda Annabi Muhammad (SAW) yana Raye Amma a cikin zukatanmu. Allah ya Kara mana Kaunarsa da bin koyarwansa. Amin.

     

    07032509197

    yaseen9253@gmail.com

    Share
  • TARIHIN MANZON ALLAH ANNABI MUHAMMADU SAW KASHI NA TALATIN (30)

    TARIHIN ANNABI MUHAMMAD (SAW) Kashi na 30

     

    RASHIN LAFIYAR ANNABI (SAW) NA KARSHE A DUNIYA.

     

    Daga: Muhammad Yaseen Bin Hussain

     

    Bayan Hajjin bankwana, Annabi Muhammad (SAW) yayi wani Rashin lafiya Mai tsanani, Rashin Lafiyan yafarane tun karshen watan Safar, yayinda Rashin Lafiyan yayi tsanani sai yanemi izini wajen dukkanin Matansa cewa su yarda yayi Jinya a Dakin matarsa Sayyada Aisha, nan take suka yarje masa.

     

    Yayinda Rashin Lafiyar Ma’aiki (SAW) tayi tsanani, har takai ga baya iya fita waje, sai yayiwa Babban Sahabbinsa, Masoyinsa, Mai Gaskiya abun gaskatawa, wato Sayyidina Abubakar izini cewa ya Shugabanci mutane a Sallah.

     

    Kudubar da Annabi Muhammad (SAW) yayi ta Karshe itace wacce yayi Lokacin da Ansar (Musulman Madina) sukaji labarin tsananin Rashin Lafiya da yake fama dashi. Ansar sun taru a Masallacin Annabi Muhammad (SAW) har saida Annabi Muhammad (SAW) ya fito Sayyidina Ali, Fadl da Sayyidina Abbas suna rike dashi Yana Dogarawa dasu, suka zaunar dashi Akan Minbari.

     

    Annabi Muhammad (SAW) yayi musu Kuduba wanda yawaicu jawaban dake cikinta kirane ga Al’ummah dasu Zama masu tawakkali ga Allah (SWT), su dinga Tina Allah a dukkanin abubuwan da sukeyi, kuma su tuna cewa komai yayi farko zaiyi karshe.

     

    Ciki Hudubar harda fadinsa cewa: “Yaku mutane labari ya isomun cewa kuna tsoron mutuwar Annabinku, shin Annabawa kafin ni (Annabi Muhammad SAW) sun Dauwama ne? Kusani kaman Yadda Allah ya dauki rayukansu Nima Allah zai dauki raina. Yaku mutane kusani cewa bawani waje zanje ba, face zan hadu da Ubangiji na, nan bada jimawaba kuma zaku hadu Dani, Ina muku wasiyyah da Kuyiwa Muhajirun Alheri, kuma Muhajirun Kuyiwa Ansar Alheri…”

     

    Wannan kadan ne daga Jawabinsa (Khuduba) da yayiwa Sahabbai a Karshen rayuwarsa. Allah ya Kara mana Kaunar Annabi Muhammad (SAW) da koyi dashi cikin zancenmu da Ayyukanmu. Amin.

     

    07032509197

    yaseen9253@gmail.com

    Share
  • TARIHIN MANZON ALLAH ANNABI MUHAMMADU SAW KASHI NA ASHIRIN DA TARA (29)

    TARIHIN ANNABI MUHAMMAD (SAW) Kashi na 29

     

    HAJJIN BANKWANA

     

    Daga: Muhammad Yaseen Bin Hussain

     

    A cikin Shekara ta 10 bayan Hijiran Annabi Muhammad (SAW) daga Makka zuwa Madina, Annabi (SAW) yayi aikin Hajji na bankwana Wanda daga wannan hajjin Bai sake yin wani aikin Hajji ba (kuma kafin wannan ma baiyi wani aikin Hajji ba).

     

    Kimanin Musulmai Dubu Chasa’in 90,000 ne sukayi wannan Hajjin tare da Annabi Muhammad (SAW), A ranar yanka Ma’ana ranar Sallan Laiha, Annabi Muhammad (SAW) yayi Huduba Wanda yayi bankwana wa mutanen Duniya Baki daya.

     

    A cikin Hudubarsa ta bankwana, Annabi Muhammad (SAW) ya Bayyana Asalin Ma’anar Addinin Musulunci, Abunda ya kunsa na Ibada da Mu’amala.

     

    Ciki harda fadinsa cewa: Haramun ne Kashe Ɗan Adam, kwace masa Dukiya ko wani abu daya Mallaka. Yace kuma, Musani cewa Matanmu sunada Hakki a kanmu, muma munada Hakki a Kansu, Musulmai ƴan uwan juna ne, Dukiyar Musulmi bata halatta ga waninsa Saida Amincewar Mai Dukiyar.

     

    Annabi Muhammad (SAW) yace: Musani cewa Daukanmu daga Annabi Adam (A.S) muke, shikuma Annabi Adam (A.S) daga Ƙasa Allah ya halicceshi. Bawanda yafi wani girma a wajen Allah (SWT) sai Wanda yafi wani Tsoron Allah, Balarabe baifi bakar fata a wajen Allah ba, sai dai Idan yafishi tsoron Allah.

     

    Wannan kadan daga cikin Hudubar tasa Kenan ta bankwana. insha’Allah zan kawo muku fassarar Hudubar nan gaba kadan Idan na gama Wannan tarihi.

     

    Allah ya taimakemu ya biya mana bukatunmu Alfarman Annabi Muhammad (SAW). Amin

     

    07032509197

    yaseen9253@gmail.com

    Share
  • TARIHIN MANZON ALLAH ANNABI MUHAMMADU SAW KASHI NA ASHIRIN DA TAKWAS (28)

    TARIHIN ANNABI MUHAMMAD (SAW) Kashi na 28.

     

    YAƘIN HUNAIN

     

    Daga: Muhammad Yaseen Bin Hussain

     

    Bayan Fathu Makkah akayi Yakin Hunain. Kabilar Saqeef da Huwazin da wasu kananan Kabilu dake goyamusu baya sune suka yanke hukunci domin su yaki Annabi Muhammad (SAW) da Musulmai kafin Da’awar Musulmai ta iso Kansu idan basuyi Imani ba, a murkushesu a yaƙesu, shine sukace bari su yaƙi musulunci kafin a yaƙesu.

     

    Kabilun sunada Mayaka kwararru masu Dunbin yawa, suka yi gangami na musamman domin wannan yakin. Annabi Muhammad (SAW) da Mayaka Dubu Goma 10,000 ne suka taso daga Madina, daga Makka kuma Musulmai Dubu Biyu 2,000 wasu Malamai sukace 1,000 ne daga Wandanda suka Musulunta ranar Fathu Makkah.

     

    Da isar Annabi Muhammad (SAW) da Sahabbansa wajen yaƙin (Hunain), sai aka fara musu ruwan kibiya, Ashe Kafiren sunyi kwanto a tsakanin Duwarwatsu, dama Kafiren sun riga Musulmai isa Filin yaƙin, sai suka Shirya harin bazata ga Musulmai.

     

    Aka fafata a Fagen daga, har Saida aka danna Musulmai, suna komawa baya, har Saida ya kasance bakowa tare da Annabi Muhammad (SAW) sai Manyan Sahabbai, Annabi Muhammad (SAW) yana Kan Alfadarinsa Mai suna Dul-Dulu ya Danna cikin Kafiren Yana cewa “Tabbas Nine Annabi Tabbas Nine Dan Abdullahi Dan Abdul-Mutallib…”

     

    Annabi Muhammad (SAW) ya durkusar da Alfadarinsa, ya Debi Kasa da hannunsa Mai Albarka ya watsawa Kafurai Makiya Allah, sai dukkan su Kasa ya shiga Idanuwansu basa gani, Sayyidina Abbas yayi Kira ga Musulmai cewa adawo Fagen daga, da yunkurowar Musulmai sai sukabi takan Kafiren da Sara da suka, aka Kashe dayawa daga cikin Kafurai aka kama Fursinonin yaki da yawa, aka samu ganiman yaki Mai yawa.

     

    Allah ya Kara daukaka Addinin Musulunci da Musulmai ya Kaskanta Kafurci da Kafurai Albarkacin Annabi Muhammad (SAW). Amin.

     

    07032509197

    yaseen9253@gmail.com

    Share
  • TARIHIN MANZON ALLAH ANNABI MUHAMMADU SAW KASHI NA ASHIRIN DA BAKWAI (27)

    TARIHIN ANNABI MUHAMMAD (SAW) Kashi na 27

     

    YAƘIN BUDE MAKKAH (Fathu Makkah)

     

    Daga: Muhammad Yaseen Bin Hussain

     

    Cikin Shekara ta 8 bayan Hijiran Annabi Muhammad (SAW) daga Makka zuwa Madina, Kafiren Makka suka janye Kan sharudan Sulhu Hudaibiyyah. janyewarsu keda wuya, sai karfin Musulmai ya karu.

     

    Annabi Muhammad (SAW) ya tinkaro Garin Makka da Kimanin Mayaka Dubu Goma 10,000. Yayinda labari ya isawa Kafiren, sukaga Bazasu iya yaƙi da Musulmai ba saboda yawansu, dayawa daga cikinsu sai suka Musulunta cikinsu harda Sarkin Makkah na wannan lokacin wato Abu-Safiyanu.

     

    Cikin Zikiri Sahabbai suka Shiga Garin Makka bayan Anyi Shela an sanarda Mutanen Makka cewa duk wanda yashiga Gidan Abu-Safiyanu ya tsira, duk Wanda yashiga Gidansa baiyi niyyan fada ko yaƙar musulmai ba shima yatsira, Amma duk Wanda yafito da Niyyan yayi faɗa ko tawaye ga Musulmai to a bakin ransa.

     

    Yayinda Annabi Muhammad (SAW) ya shiga garin Makka sai yayi Dawafi sannan ya Shiga Dakin Ka’abah ya Rusa Dukkanin abubuwan bautarsu da Gumakan da Kafiren Makka ke bautawa (wato gumaka 360 dinnan da suke dakin Ka’bah), Sai sahabban Annabi Muhammad (SAW) Suma sukayi Dawafi akayi ta Shela acikin Makka cewa ‘Gaskiya ta bayyana, Karya ta gushe. (Ja’al haq wa Zahaqal Baɗil)

     

    Daga wannan Lokacin yazama Musulunci ya tsaya da kafafunsa, Musulmai a Garin Makka da Madina da Sauran garuruwa suna Addinin su cikin daular Larabawa cikin kwanciyar hankali.

     

    Allah ya kara wa Addinin Musulunci Da Musulmai nasara, Allah ya kara mana istiqama da yaqini cikin janibin Annabi Muhammad (SAW) Amin.

     

    07032509197

    yaseen9253@gmail.com

    Share
Back to top button