TARIHIN SHEIKH TIJJANI

  • Takaitaccen Tarihin Sheikh Ahmadu Tijjani RA (Cikamakin Waliyai) Kashi Na Bakwai 7

    CIKAMAKIN WALIYAI (7)

     

    TAFIYAR SA ZUWA FAS

     

    Hijira tana shekara 1171 (1757/58 Miladiyya) Shehu Ahmadu Tijjani RTA ya cirata daga Aini Madhi zuwa birnin Fas/Fez, a lokacin shekarun sa 21. Wannan birni ya kasance babban birni mai dauke da tarihin malamai da waliyai shahararru a ƙasar Morocco, musamman saboda babban jami’ar ilimin nan da ake kira “Masjidil Ƙarawin/Jami’atul Ƙarawin” wanda wata baƙuraishiya mai suna Fatima Alfihiri ta assasa a shekarar 857/858 (miladiyya).

     

    Shehu Tijjani ya ziyarci waliyan dake cikin fas domin neman albarkar su, sannan ya ilimantu sosai daga abinda ake koyarwa a jami’ar da ma wasu masallatai da zawiyoyi a fas. Shehu Tijjani bai taɓa gajiya da sha’anin ilimi ba, yana cewa ilimi ya rabu kashi hudu kamar haka:

     

    1. Ilimi mai karfafa zuciya, wato ilimin fikihu.

    2. Ilimi mai sa a kwaɗaitu da ilimi, wato ilimin nahawu da ire-iren shi.

    3. Ilimi mai sa a fahimci rayuwar duniya, shine ilimin tarihi da abinda ya shafe shi.

    4. Ilimi mai raya zuciya, wato ilimin hadisi da duk abinda aka samo daga gareshi.

    Shiyasa Shehu Tijjani yake son abinda ya shafi hadisi sosai.

     

    A zaman sa a fas, ya mu’amalantu da waliyai guda shida, daga cikin su akwai Sheikh Ɗayyib ɗan Muhammad RTA wanda ya bashi Ɗariqar Wazaniyya wanda ake yiwa lakabi da “Ɗariqar Ɗayyibiyya Shazaliyya”, asalin darikar daga Jazuliyya ne, shehin yaso ya ƙaddamar da Shehu Tijjani amma Shehu Tijjani bai yarda ba.

     

    Sannan ya mu’amalantu da Sheikh Ahmad Saƙ-li RTA wanda ya kasance babban ƙuɗubi a Ɗariƙar Halwatiyya amma ance shehu Tijjani bai karɓi Darikar ba, wasu kuma sunce ya karɓa. Sannan ya karɓi Ɗariƙar Ƙadiriyya a wurin mukaddamin ta na wancan lokacin a fas, kuma ya karbi Ɗarikar Nasiriyya a wurin Sheikh Muhammad ɗan Abdullahi RTA wanda ake kira “Rifi”. Kuma ya karbi Ɗariƙar Sheikh Ahmad Habib RTA wanda ake kira “Al Gamari” daga wurin muqaddamin Ɗarikar na wancan lokacin, sannan shehin Ɗariƙar wato Sheikh Ahmad ya bayyana ga Shehu Tijjani a cikin mafarki ya bashi wani ismul A’azam.

     

    ✍️ Sidi Sadauki

    Share
  • Takaitaccen Tarihin Sheikh Ahmadu Tijjani RA (Cikamakin Waliyai) Kashi Na Shida 6

    CIKAMAKIN WALIYAI (6)

     

    AUREN SA DA RASUWAR IYAYEN SA

     

    Mahaifin Shehu Tijjani ya nema masa auren mace yar mutanen kirki mai cikakken tarbiyya a lokacin da ya zama matashi (ya balaga) domin ya tsare masa mutuncin sa da kuma samun rinjaye akan sharrin shaiɗan. A gidan mahaifinsa ya zauna da matar tasa cike da soyayya da begen juna. Kwatsam watarana a cikin shekarar 1166, a lokacin Shehu Tijjani yana da shekaru goma sha shida da haihuwa, cutar annoba ta kama mahaifi da mahaifiyar sa suka rasu tare, ance yini daya ne tsakanin su, Allah ya jaddada musu rahmah, Amin.

     

    Shehu Ibrahim Niasse RTA yana cewa:

    طَلَّقَ الشَّـيْخُ زَوْجَهُ إِذْ رَآهــَا * وَافَـقَـتْـهُ فِـي جِـدِّهِ الغَـيْدَاءُ

    Shehu Tijjani ya saki matar sa a lokacin da ya ga kyanta na gogayya da himmar sa.

     

    Wato Shehu Tijjani RTA yana zaune da matar sa lafiya lau amma sai ya ga akwai alamun himmar sa zata tawaya saboda dole ya raba lokacin sa na ibada da karantarwa ya ba matar tasa, bugu da ƙari can cikin zuciyar sa bashi da burin da ya wuce yayi tafiye-tafiye cikin duniya domin saduwa da manyan waliyai saboda ya riski abinda yake da buri na sha’anin yardar Allah.

     

    Don haka watarana sai ya kira matar tasa ya nemi iznin ta akan ta yarda ya sauwaƙe mata (ya sake ta) saboda burin sa ba zai bashi damar sauke mata hakkokin ta na aure ba tunda tafiye-tafiye zai yi. Da yake mace ce mai albarka da fahimta saboda tarbiyar da ta samu, sai ta yarda kuma ta karɓi uzurin sa, ya bata dukiya mai yawa a matsayin kyautatawa gareta sannan ya sake ta saki daya kuma har zuwa lokacin rabuwar su, basu haihu ba.

     

    Tarihi ya tabbatar sanadin wannan dukiyar ne matar da zuri’ar ta suka shahara fagen arziki saboda yawan sa da kuma albarkar Shehu Tijjani RTA.

     

    ✍️ Sidi Sadauki

    Share
  • Tarihin Rayuwar Sheikh Ahmadu Tijjani RA (Cikamakin Waliyai) Kashi Na Shida 6.

    CIKAMAKIN WALIYAI (6)

     

    AUREN SA DA RASUWAR IYAYEN SA.

     

    Mahaifin Shehu Tijjani ya nema masa auren mace yar mutanen kirki mai cikakken tarbiyya a lokacin da ya zama matashi (ya balaga) domin ya tsare masa mutuncin sa da kuma samun rinjaye akan sharrin shaiɗan. A gidan mahaifinsa ya zauna da matar tasa cike da soyayya da begen juna. Kwatsam watarana a cikin shekarar 1166, a lokacin Shehu Tijjani yana da shekaru goma sha shida da haihuwa, cutar annoba ta kama mahaifi da mahaifiyar sa suka rasu tare, ance yini daya ne tsakanin su, Allah ya jaddada musu rahmah, Amin.

     

    Shehu Ibrahim Niasse RTA yana cewa:

    طَلَّقَ الشَّـيْخُ زَوْجَهُ إِذْ رَآهــَا * وَافَـقَـتْـهُ فِـي جِـدِّهِ الغَـيْدَاءُ

    Shehu Tijjani ya saki matar sa a lokacin da ya ga kyanta na gogayya da himmar sa.

     

    Wato Shehu Tijjani RTA yana zaune da matar sa lafiya lau amma sai ya ga akwai alamun himmar sa zata tawaya saboda dole ya raba lokacin sa na ibada da karantarwa ya ba matar tasa, bugu da ƙari can cikin zuciyar sa bashi da burin da ya wuce yayi tafiye-tafiye cikin duniya domin saduwa da manyan waliyai saboda ya riski abinda yake da buri na sha’anin yardar Allah.

     

    Don haka watarana sai ya kira matar tasa ya nemi iznin ta akan ta yarda ya sauwaƙe mata (ya sake ta) saboda burin sa ba zai bashi damar sauke mata hakkokin ta na aure ba tunda tafiye-tafiye zai yi. Da yake mace ce mai albarka da fahimta saboda tarbiyar da ta samu, sai ta yarda kuma ta karɓi uzurin sa, ya bata dukiya mai yawa a matsayin kyautatawa gareta sannan ya sake ta saki daya kuma har zuwa lokacin rabuwar su, basu haihu ba.

     

    Tarihi ya tabbatar sanadin wannan dukiyar ne matar da zuri’ar ta suka shahara fagen arziki saboda yawan sa da kuma albarkar Shehu Tijjani RTA.

     

    ✍️ Sidi Sadauki

    Share
  • Tarihin Rayuwar Sheikh Ahmadu Tijjani RA (Cikamakin Waliyai) Kashi Na Biyar 5.

    CIKAMAKIN WALIYAI (5)

     

    TASOWAR SA DA NEMAN ILIMIN SA

     

    Ko ban faɗa ba, mai karatu zai gane cewa duk wanda Allah ya azurta da irin wayannan iyaye, dole ya samu cikakken kulawa na ilimi da tarbiya, haka ne ya kasance ga Shehu Tijjani kuwa, domin bayan ya tasa kaɗan, sai iyayen sa suka mika shi gun babban waliyyi mai suna Sayyidi Abi-Abdallah Muhammad ɗan Hamu Almadawiy (ya rasu 1162H) domin yayi karatu, kuma cikin ikon Allah ya haddace Alqur’ani bisa ruwayar warshu a hannun sa yana da shekaru bakwai a duniya.

     

    Wannan malamin na Shehu Tijjani, ya sadaukar da lokacin sa wurin ilimantar da yara da manya, kuma ya gaji haka ne daga wurin malamin sa wanda yake babban waliyyi mai suna Sheikh Isa Bu’akaz Almadawi RTA wanda ya ga Allah (SWT) a mafarki (ru’uya), ya karantawa Allah Alqur’ani mai girma a ruwayar warshu, Allah yace “masa tabbas haka aka saukar da shi, babu abinda ka rage ko ka ƙara”.

     

    Allahu Akbar!

     

    Shehu Ahmad Tijjani ya karanta littattafan fiƙihu da na furu’a da adab da sauran su tun daga kan su Ahalari, Ishmawiy, Risala, Ibn Rushid da sauran su a wurin babban waliyyi masanin Allah mai suna Sidi Mubarak Bu’afiya Almadawiy RTA.

     

    Watarana Shehu Ahmad Tijjani RTA ya fito daga aji sai yaga haske daga ƙasa zuwa samaniya, sai Annabi SAW ya bayyana, yace masa “Cigaba da juriya, kana kan tafarki madaidaiciya “, Shehu Tijjani ya tsorata matuƙa, ya ruga wurin gwaggon sa mai suna “Jurkhum” ya faɗa mata sai ta kwantar mai da hankali ta bashi abincin da yake so. Shehu Tijjani yana son Jurkhum sosai kuma daga baya ya faɗi cewa waliyiya ce babba wacce babu abinda mutum zai tsaya kan kabarin ta ya roki Allah shi, na sharri ko alheri, face sai Allah ya amsa masa, dalilin haka aka daina nuna kabarin nata har ya bace.

     

    Kafin Shehu Ahmadu Tijjani RTA ya cika shekaru ashirin da daya a duniya, ya gama da duk wani ilimi na littafi na ilimin Shari’a da Sufanci. Ilimin Shehu Tijjani da yadda yake saurin fahimtar abubuwa da haddace su, kyauta ce daga Allah, babu tamkar sa a cikin abokan karatun sa, babu wani abu da zai sa a gaba bai cimma karshen sa ba, ba shi da karaya ko tsoro ko fargaba ko kaɗan, duk da shekarun sa kadan ne, amma ya tara ilimi na ban mamaki kuma tuni labarin ilimin ya sa mamaye garuruwan dake kusa da Ainu Madhi har ma akan zo gareshi domin neman ƙarin bayani da fatawa.

     

    ALLAH KA AZURTA MU DA ILIMI MAI AMFANI IRIN NA SHEHU TIJJANI, KAYI MANA TSARI DA ILIMI MARA AMFANI WANDA YAKE SA A ZAGI SHEHU TIJJANI RTA.

     

    ✍️ Sidi Sadauki

    Share
  • Tarihin Rayuwar Sheikh Ahmadu Tijjani RA (Cikamakin Waliyai) Kashi Na Hudu 4.

    CIKAMAKIN WALIYAI (4)

     

    IYAYE DA YAN’UWANSA (RTA)

     

    Mahaifin Shehu Ahmad Tijjani wato Sayyidi Muhammad (RTA) ya kasance babban malami masanin Alqur’ani da Sunna kuma mai matukar kiyaye umurni da hanin Allah, mai kokarin kiran halittun Allah zuwa ga tafarkin shiriya, ya rayu bisa cin halal tsantsa, yawan zikiri da ibadu daban-daban, ya samu yardar Allah (wulaya) har ma rauhanai sukan ziyarce shi da kyautar dukiya da abubuwa daban-daban amma sai ya ce su tafi, shi baya bukatar komai daga wurin halitta sai dai daga wurin mahalicci.

     

    Mahaifiyar Shehu Ahmad Tijjani kuwa wato Sayyida Aisha (RTA), mace ce mai tsarkin nasaba kamar yadda muka kawo a baya, ta samu cikakken tarbiyya da ilimin addini daga iyayen ta, kuma sai Allah ya aura mata waliyyi a matsayin miji, shiyasa ta rayu ita ma bisa abinda mijin nata yake kai na ibada cike da tsoron Allah.

     

    Ta haifi yara da yawa suna mutuwa a ƙananan shekaru amma bata yi baƙin cikin haka ba domin ta yarda Allah ke bayarwa kuma ya karɓa a lokacin da yaso domin ya jarrabi imanin bayin sa. Daga karshe Allah sai ya raya mata yar ta mace mai suna Rukayya, sannan ta haifi Shehu Ahmad Tijjani, kana daga bisani tayi masa ƙani mai suna Muhammad wanda ake yi masa laƙabi da Ibn Umar.

     

    Allah ya kara musu yarda, Amin!

     

    ✍️ Sidi Sadauki

    Share
Back to top button