HANYOYI GUDA ASHIRIN DA BIYAR (25) NA SAMUN SHIGA ALJANNAH!.

HANYOYI GUDA ASHIRIN DA BIYAR (25) NA SAMUN SHIGA ALJANNAH!

 

1. ANNABI (S.A.W) yace : ”Duk wanda ya hina ma Allah Masallaci, to Allah zai gina masa gida a cikin Aljannah. (Bukhari da kuma, Tirmidhi hadisi na 318)

 

2. ANNABI (S.A.W) Yace : ”Wanda yayi Salloli biyu na sanyi (Sallar La’asar da Sallar Asuba) zai shiga Aljannah. ” (Bukhari)

 

3. An karbo Hadisi daga Abu Hurairah (RA) yace : ANNABI (S.A.W) Yace : ”Duk wanda yace : ”SUBHANALLAHI WABIHAMDIHI, SUBHANALLAHIL-AZEEM.” Sau bakwai (7)

za’a gina masa bene a cikin Aljannah.

”Al-wabilus Sayyib Shafi na 77.”

 

4. Jabir, Allah ya yarda dashi, yace: ANNABI (S.A.W) Yace : ”Wanda yace ”SUBHANALLAHIL -AZEEM WA BIHAMDIHI. ” za’a dasa masa bishiyar Dabino a cikin Aljannah.”

 

5. ANNABI (S.A.W) Yace : ”Duk Wanda Qarshen Maganarsa ta kasance ”LA’ILAHA ILLALLAH.” zai shiga Aljannah.” (Abu Dawud)

 

6. ANNABI (S.A.W) Yace : ”Duk wanda Yace : ”Ya Allah Ina Rokonka, ka Shigar dani Aljannah sau ukku (3) (Allahumma Inniy As’alukal jannah) ALJANNAH ZA TA CE : ”Ya Allah ka shigar dashi Aljannah.” (Tirmiziy ne ya ruwaita shi)

 

7. ANNABI (S.A.W) Yace : ”Ya ku Mutane ku watsa Sallama, kuma ku ciyarda da Abinci ga mai jin yunwa, kuma kuyi Sallah lokacin da Mutane ke bacci (da dare) sai ku shiga Aljannah da Aminci.” (Tirmiziy ne ya ruwaito shi)

 

8. ANNABI (S.A.W) Yace : ”Lallai Allah yanada sunaye sasa’in da tara (99), Duk wanda yasan Ma’anar su kuma ya kiyayesu Zai shiga Aljannah (Bukhari)

 

9. ANNABI (S.A.W) Yace : ”Wa zai Lamunce min Abinda ke tsakanin Habobinsa guda biyu da kuma Abinda ke tsakanin kafafunsa biyu (Wato : Harshen sa da kuma Farjinsa) In Lamunce masa Shiga Aljannah.”

(Sahih Bukhari )

 

10. An kar6o Hadisi daga Aisha (RAH) tace : ANNABI (S.A.W) Yace : ”Duk wanda ya ga wata kafa a cikin Sahu kuma ya toshe, Allah zai gina Masa gida a cikin Aljannah kuma zai daukaka darajarsa a cikin Aljanna.’

 

Allah yasa mu dace. Amiin

Share

Back to top button